Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 69 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Kukan Neman Taimako

1. Ka cece ni, ya Allah!Ruwa ya sha kaina.

2. Ina nutsewa cikin laka mai zurfi,Ba kuwa ƙasa mai ƙarfi,Na tsunduma cikin ruwa mai zurfi,Raƙuman ruwa kuwa sun kusa kashe ni.

3. Na gaji da kira, ina neman taimako,Maƙogwarona yana yi mini ciwo,Idanuna duka sun gaji,Saboda ina zuba ido ga taimakonka.

4. Waɗanda suke ƙina ba daliliSun fi gashin kaina yawa,Waɗanda suke baza ƙarya suke ƙina,Suna da ƙarfi, suna kuwa so su kashe ni.Suka tilasta ni in mayar da abubuwan da ba satarsu na yi ba.

5. Zunubaina ba a ɓoye suke a gare ka ba ya Allah,Ka san irin wawancin da na yi!

6. Kada ka bar ni in jawo kunya ga waɗanda suka dogara gare ka,Ya Ubangiji Allah Mai Iko Dukka!Kada ka bar ni in jawo abin kunyaGa waɗanda suke maka sujada, ya Allah na Isra'ila!

7. Sabili da kai ne aka ci mutuncina,Kunya ta rufe ni.

8. Kamar baƙo nake ga 'yan'uwana,Haka ma ga iyalina, kamar baƙo nake.

9. Ƙaunar da nake da ita ta yin ibada a HaikalinkaTana iza ni a ciki kamar wuta,Zargin da suke yi a kanka, ya fāɗa a kaina.

10. Na ƙasƙantar da kaina ta wurin yin azumi,Jama'a kuwa suka ci mutuncina.

11. Na sa tufafin makoki,Sai suka maishe ni abin dariya.

12. A tituna suna ta magana a kaina,Bugaggu da giya kuwa suna raira waƙa a kaina.

13. Amma ni, zan yi addu'a gare ka, ya Ubangiji,Ka amsa mini, ya Allah, a lokacin da ka zaɓa,Sabili da muhimmiyar ƙaunarka,Saboda kana cika alkawarinka na yin ceto.

14. Ka cece ni daga nutsewa cikin wannan laka,Ka kiyaye ni daga maƙiyana,Daga kuma wannan ruwa mai zurfi.

15. Kada ka bar ambaliyar ruwa ta rufe ni.Kada ka bar ni in mutu cikin zurfafa,Ko in nutse a cikin kabari.

16. Sabili da madawwamiyar ƙaunarka, ka amsa mini, ya Ubangiji,Ka juyo wurina, saboda juyayinka mai girma!

17. Kada ka ɓoye kanka daga bawanka,Ina shan babbar wahala, ka yi hanzari ka amsa mini!

18. Ka zo ka fanshe ni,Ka kuɓutar da ni daga abokan gābana.

19. Ka san yadda ake cin mutuncina,Da yadda ake kunyata ni, ake ƙasƙantar da ni,Kana ganin dukan abokan gābana.

20. Zuciyata ta karai saboda cin mutuncin da ake ci mini,Ni kuwa ba ni da mataimaki,Na sa zuciya za a kula da ni,Amma babu.Na sa zuciya zan sami ta'aziyya,Amma ban samu ba.

21. Sa'ad da na ji yunwa, sai suka ba ni dafi,Sa'ad da na ji ƙishi, sai suka ba ni ruwan tsami.

22. Allah ya sa bukukuwansu su zama lalacewarsu,Shagulgulansu kuma su zama sanadin fāɗuwarsu!

23. Ka makantar da su, har da ba za su iya gani ba,Kullum ka sa bayansu ya ƙage!

24. Ka kwarara musu fushinka,Bari zafin fushinka ya ci musu!

25. Allah ya sa su gudu su bar sansaninsu,Kada wani ya ragu da rai cikin alfarwansu!

26. Sun tsananta wa waɗanda ka hukunta,Suna taɗin shan wuyar waɗanda ka aukar wa cutar.

27. Ka riɓaɓɓanya zunubansu,Kada ka bar su su sami rabon kome daga cikin cetonka.

28. Ka sa a goge sunansu daga cikin littafin rai,Kada a sa su a lissafin jama'arka.

29. Amma ni mai bukata ne, ina shan wahala,Ka tsame ni, ya Allah, ka cece ni!

30. Zan raira waƙar yabo ga Allah,Zan yi shelar girmansa ta wurin yi masa godiya,

31. Wannan zai daɗaɗa wa Ubangiji raiFiye da hadayar bijimi,Fiye da a ba shi bijimi bana bakwai.

32. Sa'ad da masu bukata suka ga wannan za su yi murna,Waɗanda suke yi wa Allah sujada kuwa za a ƙarfafa su.

33. Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata,Bai manta da jama'arsa da suke a kurkuku ba.

34. Ku yabi Allah, ku al'arshi da duniya, ku yabi Allah,Tekuna da dukan talikan da suke cikinsu!

35. Gama zai ceci Sihiyona,Ya sāke gina garuruwan Yahuza,Jama'arsa za su zauna a wurin, su mallaki ƙasar.

36. Zuriyar bayinsa za su gāje ta,Masu ƙaunarsa za su zauna a wurin.