Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 44 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Neman Ceto

1. Da kunnuwanmu muka ji, ya Allah,Kakanninmu suka faɗa mana,Manya manyan abubuwa da ka aikata a lokacinsu,A zamanin dā,

2. Yadda kai da kanka ka kori arna,Ka dasa jama'arka a ƙasarsu,Yadda ka hori sauran al'umma,Amma ka sa jama'arka su wadata.

3. Ba da takubansu suka ci ƙasar ba,Ba kuwa da ikonsu suka rinjayi ƙasar ba,Amma da ikonka ne da kuma ƙarfinka,Ta wurin tabbatar musu kana tare da su,Kana nuna musu kana ƙaunarsu.

4. “Ya Allah, kai ne Sarkina,Ka ba jama'arka nasara.

5. Da ikonka muka kori abokan gābanmu,Saboda kasancewarka tare da muMuka rinjayi magabtanmu.

6. Ban dogara ga bakana ba,Takobina kuwa ba zai cece ni ba.

7. Amma ka cece mu daga abokan gābanmu,Ka kori waɗanda suke ƙinmu.

8. Za mu yabe ka kullum,Mu yi maka godiya har abada.”

9. Amma yanzu, ya Allah, ka yashe mu,Ka bari aka kore mu,Ba ka ƙara fita ka yi tafiya tare da sojojinmu ba.

10. Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu,Suka ƙwace abin da muke da shi.

11. Ka bari aka yanyanka mu kamar tumaki,Ka warwatsar da mu a baƙuwar ƙasa.

12. Ka sayar da jama'arkaA bakin 'yan kuɗi ƙalilan,Ba ka ci ribar cinikin ba.

13. Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai,Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa.

14. Ka maishe mu abin raini a wurin arna,Suna kaɗa mana kai, suna raina mu.

15. Kullum a cikin kunya nake,Kunya ta lulluɓe ni ɗungum,

16. Saboda dukan wulakanci,Da zagin da nake sha daga maƙiyana da abokan gābana.

17. Dukan wannan ya same mu,Ko da yake ba mu manta da kai ba,Ba mu kuma ta da alkawarin da ka yi da mu ba.

18. Ba mu ci amanarka ba,Ba mu ƙi yin biyayya da umarnanka ba.

19. Duk da haka ka ƙi taimakonmu da namomin jejin nan,Ka bar mu a cikin duhu baƙi ƙirin.

20. Da a ce mun daina yin sujada ga Allahnmu,Muka yi addu'a ga gumaka,

21. Hakika ka gane,Domin ka san asirin tunanin mutane.

22. Ya Allah, saboda kai ne ake karkashe mu a kowane lokaci,Ake kuma maishe mu kamar tumakin da za a yanyanka.

23. Ka tashi, ya Ubangiji! Me ya sa kake zama kamar mai barci?Ka tashi! Kada ka yashe mu har abada!

24. Me ya sa ka ɓuya mana?Kada ka manta da ƙuncinmu da wahalarmu!

25. Mun fāɗi, an turmushe mu a ƙasa,An bar mu kwance cikin ƙura.

26. Ka tashi ka taimake mu!Ka fanshe mu saboda madawwamiyar ƙaunarka!