Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 80 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Komo da Al'umma

1. Ka kasa kunne gare mu, ya Makiyayin Isra'ila,Ka ji mu, kai da kake shugaban garkenka,Da kake zaune a kan kursiyinka, a bisa kerubobi.

2. Ka bayyana ƙaunarka ga kabilar Ifraimu,Da ta Biliyaminu, da ta Manassa!Ka nuna mana ikonka,Ka zo ka cece mu!

3. Ka komo da mu, ya Allah!Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

4. Har yaushe ke nan ya Ubangiji Allah Mai Runduna,Za ka yi ta fushi da addu'o'in jama'arka?

5. Ka ciyar da mu da hawaye,Ka shayar da mu da babban ƙoƙo na hawaye.

6. Ka bar al'umman da take makwabtaka da muSu yi ta faɗa a kan ƙasarmu,Abokan gābanmu kuma suna yi mana ba'a.

7. Ka komo da mu, ya Allah Mai Runduna!Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

8. Ka fito da kurangar inabi daga cikin Masar,Ka kori sauran al'umma,Ka dasa kurangar a ƙasarsu.

9. Ka gyara mata wuri don ta yi girma,Saiwoyinta suka shiga ƙasa sosai,Ta yaɗu, ta rufe dukan ƙasar.

10. Ta rufe tuddai da inuwarta,Ta rufe manya manyan itatuwan al'ul da rassanta.

11. Rassanta sun miƙe har Bahar Rum,Har zuwa Kogin Yufiretis.

12. Me ya sa ka rushe shingen da yake kewaye da ita?Ga shi yanzu, duk mai wucewa yana iya satar 'ya'yanta.

13. Aladen jeji kuma za su tattake ta,Namomin jeji duka za su cinye ta.

14. Ka juyo wurinmu, ya Allah Mai Runduna!Daga Sama, ka dube mu,Ka zo ka ceci kurangar inabinka!

15. Ka zo ka ceci kurangar inabin nanWadda kai da kanka ka dasa,Wannan ƙaramar kuranga,Ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!

16. Abokan gābanmu sun sa mata wuta, sun sare ta,Ka yi fushi da su, ka hallaka su!

17. Ka kiyaye jama'arka wadda ka zaɓa,Ka keɓe ta.Al'umman nan wadda ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!

18. Ba za mu ƙara rabuwa da kai ba,Ka rayar da mu, mu kuwa za mu yabe ka.

19. Ka komo da mu, ya Ubangiji Allah Mai Runduna!Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!