Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 118 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Godiyar domin Cin Nasara

1. Ku gode wa Ubangiji,Domin shi mai alheri ne,Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.

2. Bari jama'ar Isra'ila su ce,“Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.”

3. Bari dukan firistoci na Allah su ce,“Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.”

4. Bari dukan waɗanda suke tsoronsa su ce,“Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.”

5. A cikin wahalata na yi kira ga UbangijiYa kuwa amsa mini, ya kuɓutar da ni.

6. Ubangiji yana tare da ni, ba zan ji tsoro ba.Me mutane za su iya yi mini?

7. Ubangiji ne yake taimakona,Zan kuwa ga fāɗuwar maƙiyana da idona.

8. Gwamma a dogara ga Ubangiji,Da a dogara ga mutane.

9. Gwamma a dogara ga Ubangiji,Da a dogara ga shugabanni na mutane kawai.

10. Ma ƙiya da yawa sun kewaye ni,Amma na hallaka su ta wurin ikon Ubangiji!

11. Suka kewaye ni a kowane gefeAmma na hallaka su ta wurin ikon Ubangiji!

12. Suka rufe ni kamar ƙudan zuma,Amma suka ƙone nan da nan kamar wutar jeji,Ta wurin ikon Ubangiji na hallaka su!

13. Aka auko mini da tsanani,Har aka kore ni,Amma Ubangiji ya taimake ni.

14. Ubangiji yakan ba ni iko, ya ƙarfafa ni,Shi ne Mai Cetona!

15. Ku kasa kunne ga sowar murna ta nasaraA cikin alfarwan jama'ar Allah.“Ikon Ubangiji mai girma ne ya aikata wannan!

16. Ikonsa ne ya kawo mana nasara,Babban ikonsa a wurin yaƙi!”

17. Ba zan mutu ba, amma rayuwa zan yi,Don in ba da labarin abin da Ubangiji ya yi.

18. Ya hukunta ni da hukunci mai tsanani,Amma bai kashe ni ba.

19. A buɗe mini ƙofofin Haikali,Zan shiga ciki in yabi Ubangiji!

20. Wannan ƙofar Ubangiji ce,Sai adalai kaɗai suke shiga ciki!

21. Ina yabonka, ya Ubangiji, domin ka ji ni,Domin ka ba ni nasara!

22. Dutsen da magina suka ƙi, wai ba shi da amfani,Sai ya zama shi ya fi duka amfani.

23. Ubangiji ne ya yi haka,Wannan kuwa abin banmamaki ne!

24. Wace irin rana ce haka da Ubangiji ya ba mu!Bari mu yi farin ciki, mu yi biki!

25. Ka cece mu, ya Ubangiji, ka cece mu!Ka ba mu nasara, ya Ubangiji!

26. Allah yakan sa wa wanda ya zo da sunan Ubangiji albarka!Daga Haikalin Ubangiji muke yabonka!

27. Ubangiji shi ne Allah, yana yi mana alheri,Ku ɗauki hadayunku ku yi ta idi,Ku ɗaura su a zankayen bagade.

28. Kai ne Allahna, kai nake yi wa godiya,Zan yi shelar girmanka.

29. Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne,Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.