Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 32 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Albarkar Gafarar Zunubi

1. Mai farin ciki ne mutumin da aka gafarta masa zunubansa,Mai farin ciki ne kuma wanda aka gafarta masa laifofinsa.

2. Mai farin ciki ne wanda Ubangiji bai zarge shi a kan wani laifi ba,Wanda ba algus ko kaɗan a cikinsa.

3. Sa'ad da ban hurta zunubaina ba,Na gajiyar da kaina da yawan kuka dukan yini.

4. Ka hukunta ni dare da rana, ya Ubangiji,Ƙarfina duka ya ƙare sarai,Kamar yadda laima yake bushewa,Saboda zafin bazara.

5. Sa'an nan na hurta zunubaina gare ka,Ban ɓoye laifofina ba.Na ƙudurta in hurta su gare ka,Ka kuwa gafarta dukan laifofina.

6. Saboda haka dukan jama'arka masu biyayya,Za su yi addu'a gare ka, lokacin bukata.Sa'ad da babbar rigyawa ta malalo,Ba za ta kai wurinsu ba.

7. Kai ne maɓoyata,Za ka cece ni daga wahala.Ina raira waƙa da ƙarfi saboda cetonka,Domin ka kiyaye ni.

8. Ubangiji ya ce, “Zan koya maka hanyar da za ka bi,Zan koya maka, in kuma ba ka shawara.

9. Kada ka zama wawa kamar doki ko alfadari,Wanda dole sai da linzami, da ragama za a sarrafa shi,Sa'an nan yă yi maka biyayya.”

10. Tilas ne mugu yă sha wahala,Amma masu dogara ga Ubangiji,Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su.

11. Dukanku adalai, ku yi murna,Ku yi farin ciki,Saboda abin da Ubangiji ya yi!Dukanku da kuke yi masa biyayya,Ku yi sowa ta farin ciki!