Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 95 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Waƙar Yabo da Sujada

1. Ku zo mu yabi Ubangiji!Mu raira waƙa domin farin ciki ga mai kiyaye mu,Da Mai Cetonmu!

2. Mu zo gabansa da godiya,Mu raira waƙoƙin farin ciki na yabo!

3. Gama Ubangiji Allah ne mai iko,Shi yake mulki bisa sauran alloli duka.

4. Yana mulki bisa dukan duniya,Daga zurfafan kogwannin duwatsu zuwa tuddai mafiya tsayi.

5. Yana mulki bisa tekun da ya yi,Da kuma bisa ƙasar da ya siffata.

6. Ku zo, mu durƙusa, mu yi masa sujada,Mu durƙusa a gaban Ubangiji, Mahaliccinmu!

7. Shi ne Allahnmu,Mu ne jama'ar da yake lura da ita,Mu ne kuma garken da yake ciyarwa.Yau ku ji abin da yake faɗa.

8. “Kada ku taurare zuciyarku yadda kakanninku suka yi a Meriba,Kamar yadda suka yi a jeji a Masaha, a wancan rana.

9. A can suka gwada ni suka jarraba ni,Ko da yake da idanunsu suka ga abin da na yi dominsu.

10. A shekara arba'in ɗin nan,Jama'ar nan ta zama abar ƙyama gare ni,‘Su marasa biyayya ne,’ in ji ni,‘Gama sun ƙi bin umarnaina!’

11. Sai na ji haushi, na yi musu alkawari mai nauyi.Na ce, ‘Faufau ba za ku shiga ƙasar da zan ba ku hutawa a ciki ba.’ ”