Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 116 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Mutumin da aka Cece shi daga Mutuwa

1. Ina ƙaunar Ubangiji, saboda yana jina,Yana kasa kunne ga addu'o'ina.

2. Yakan kasa kunne gare ni,A duk lokacin da na yi kira gare shi.

3. Mutuwa ta ɗaure ni da igiyarta tam,Razanar kabari ta auka mini,Na cika da tsoro da alhini.

4. Sa'an nan sai na yi kira ga Ubangiji, na ce,“Ina roƙonka, ya Ubangiji, ka cece ni!”

5. Ubangiji mai jinƙai ne, mai alheri,Allahnmu mai rahama ne.

6. Ubangiji yakan kiyaye kāsassu,Sa'ad da na shiga hatsari ya cece ni.

7. Kada ki yi shakka, ya zuciyata,Gama Ubangiji yana yi mini alheri.

8. Ubangiji ya cece ni daga mutuwa,Ya share hawayena,Bai bari a kāshe ni ba.

9. Don haka nake tafiya a gaban UbangijiA duniyar masu rai.

10. Na dai yi ta gaskatawa, ko da yakeNa ce, “An ragargaza ni sarai.”

11. Sa'ad da na ji tsoro na ce,“Ba wanda za a iya dogara gare shi.”

12. Me zan bayar ga UbangijiSaboda dukan alheransa gare ni?

13. Zan miƙa hadaya ta sha ga Ubangiji,Ina gode masa domin dā ya cece ni.

14. Zan ba shi abin da na alkawartaA taron dukan jama'arsa.

15. Mutuwar ɗaya daga cikin tsarkakansa,Abu mai daraja ne!

16. Ni bawanka ne, ya Ubangiji,Ina bauta maka yadda mahaifiyata ta yi,Ka 'yantar da ni.

17. Zan miƙa maka hadaya ta godiya,Zan yi addu'ata a gare ka.

18-19. A taron dukan jama'arka,A shirayun Haikalinka,A Urushalima, zan ba ka abin da na alkawarta.Yabo ya tabbata ga Ubangiji!