Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 83 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'a don A Hallaka Abokan Gāban Isra'ila

1. Ya Allah, kada ka yi shiru,Kada ka tsaya cik,Ya Allah, kada kuma ka yi tsit!

2. Duba, abokan gābanka suna tawaye,Maƙiyanka sun tayar.

3. Suna ta ƙulle-ƙulle a asirce gaba da jama'arka,Suna shirya maƙarƙashiya gāba da waɗanda kake tsaronsu.

4. Suna cewa, “Ku zo, mu hallakar da al'ummarsu,Don a manta da Isra'ila har abada!”

5. Suka yarda a kan abin da suka shirya,Suka haɗa kai gāba da kai.

6. Su ne mutanen Edom, da Isma'ilawa,Da mutanen Mowab, da Hagarawa,

7. Da mutanen Gebal, da na Ammon, da na Amalek,Da na Filistiya, da na Taya.

8. Assuriya ma ta haɗa kai da su,Haɗa kai ke nan mai ƙarfi da zuriyar Lutu.

9. Ka yi musu yadda ka yi wa Madayanawa,Ka yi musu yadda ka yi wa SiseraDa Yabin a Kogin Kishon,

10. Waɗanda aka kora a Endor,Gawawwakinsu kuwa suka ruɓe a ƙasa.

11. Ka yi wa shugabannin yaƙinsu yadda ka yi wa Oreb da Ziyib,Ka kori dukan masu mulkinsu yadda ka kori Zeba da Zalmunna,

12. Waɗanda suka ce, “Za mu ƙwace ƙasar da take ta Allah, ta zama tamu.”

13. Ya Allahna, ka warwatsa su kamar ƙura,Ka warwatsa su kamar ciyayin da iska take hurawa.

14. Kamar yadda wuta take cin jeji,Kamar yadda harshen wuta yake ƙone tuddai,

15. Ka runtume su da hadirinka,Ka razanar da su da iskarka mai ƙarfi.

16. Ya Ubangiji, ka sa kunya ta rufe su,Don su so su bauta maka.

17. Ka sa a kore su, a razanar da su har abada,Ka sa su mutu, mutuwar ƙasƙanci!

18. Ka sa su sani kai kaɗai ne Ubangiji,Kai kaɗai ne mamallakin dukan duniya!