Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 79 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Makoki saboda An Lalatar da Urushalima

1. Ya Allah, arna sun fāɗa wa ƙasar jama'arka!Sun ƙazantar da Haikalinka tsattsarka,Sun bar Urushalima kufai.

2. Suka bar wa tsuntsaye gawawwakin jama'arka su ci,Suka bar wa namomin jeji gawawwakin bayinka.

3. Suka zubar da jinin jama'arka kamar ruwa,Jini ya yi ta gudu kamar ruwaKo'ina a Urushalima,Ba ma wanda ya ragu don yă binne gawawwaki.

4. Sauran al'ummar da take kewaye da mu,Suka maishe mu abin ba'a, suka yi mana dariya,Suka yi mana ba'a.

5. Har yaushe za ka yi ta fushi da mu, ya Ubangiji?Har abada ne?Kullum ne fushinka zai yi ta ci kamar wuta?

6. Ka yi fushi da al'umman da ba su yi maka sujada,Ka yi fushi da jama'ar da suka ƙi ka!

7. Sun karkashe mutanenmu,Sun kuwa lalatar da ƙasarmu.

8. Kada ka hukunta mu saboda zunuban kakanninmu,Amma ka yi mana jinƙai yanzu,Gama mun fid da zuciya sarai.

9. Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu,Saboda girmanka.Ka cece mu, ka gafarta mana zunubanmu,Don mutane su yabe ka.

10. Don me al'ummai za su tambaye mu cewa,“Ina Allahnku?”Bari mu ga ka hukunta al'ummaiSaboda sun zubar da jinin bayinka!

11. Ka kasa kunne ga nishin 'yan sarƙa,Ka kuɓutar da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa,Ta wurin ikonka mai girma.

12. Ya Ubangiji, ka rama wa al'umman nan har sau bakwai,Saboda tsiwace-tsiwacen da suka yi maka.

13. Mu waɗanda muke jama'arka, tumakin garkenka,Za mu gode maka, mu yabe ka har abada.