Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 66 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Waƙar Yabo da Miƙa Hadaya ta Godiya

1. Ku yabi Allah da babbar murya ta farin ciki,Ya jama'a duka!

2. Ku raira waƙar darajar sunansa,Ku yabe shi da ɗaukaka!

3. Ku faɗa wa Allah cewa, “Al'amuran da kake aikatawaSuna da banmamaki ƙwarai!Ikonka yana da girma ƙwarai,Har maƙiyanka sukan durƙusa a gabanka don tsoro.

4. Duk wanda yake a duniya, yana yi maka sujada,Yana raira maka waƙar yabbai,Yana raira yabbai ga sunanka.”

5. Zo, ka ga abin da Allah ya yi,Ayyukansa masu ban al'ajabiWaɗanda ya aikata ga mutane.

6. Ya sa teku ta zama busasshiyar ƙasa,Kakanninmu suka haye kogi da ƙafa.A can muka yi farin ciki saboda abin da ya yi.

7. Har abada yana mulki ta wurin ƙarfinsa,Yana duban al'ummai,Don kada 'yan tawaye su tayar masa!

8. Ku yabi Allahnmu, ya ku dukan al'ummai,Bari a ji yabon da kuke yi masa.

9. Shi ne yake rayar da mu,Bai kuwa yarda mu fāɗi ba.

10. Ka jarraba mu, ya Allah,Kamar yadda ake tace azurfa da wuta,Haka nan ka jarraba mu.

11. Ka bar mu muka fāɗa a tarko,Ka ɗora mana kaya masu nauyi.

12. Ka bar maƙiyanmu suka tattaka mu,Mun ratsa ta cikin wuta da rigyawa,Amma yanzu ka kawo mu a lafiyayyen wuri.

13. Zan kawo hadayun ƙonawa a ɗakinka,Zan miƙa maka abin da na alkawarta.

14. Zan ba ka abin da na ce zan bayar,A lokacin da nake shan wahala.

15. Zan miƙa tumaki don a ƙona a kan bagade,Nan za a ji ƙanshi mai daɗi na ƙonannun awaki,Zan miƙa hadayu na bijimai da na awaki.

16. Ku zo ku ji, dukanku, ku da kuke girmama Allah,Ni kuwa zan faɗa muku abin da ya yi mini.

17. Na yi kira gare shi neman taimako,A shirye nake in yabe shi da waƙoƙi.

18. Da ban watsar da zunubaina ba,Da Ubangiji bai ji ni ba.

19. Amma hakika Allah ya ji ni,Ya saurari addu'ata.

20. Ina yabon Allah,Domin bai ƙi addu'ata ba,Bai kuwa hana mini madawwamiyar ƙaunarsa ba.