Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Neman a Yi Adalci

1. Ya Ubangiji, Allahna, na sami mafaka a wurinka,Ka cece ni, ka tserar da ni daga dukan masu fafarata,

2. Idan ba haka ba kuwa, za su ɗauke ni,Su tafi da ni zuwa wurin da ba wanda zai cece ni,A can za su yayyage ni kamar zaki.

3. Ya Ubangiji, Allahna, idan na aikata ɗaya daga cikin waɗannan,Wato idan na yi wa wani laifi,

4. Idan na ci amanar abokina,Ko kuwa in na gwada wa maƙiyi fin ƙarfi ba dalili,

5. To, bari abokan gābana su fafare ni, su kama ni,Bari su datse ni har ƙasa, su kuma kashe ni,Su bar ni ƙasa, matacce!

6. Ka tashi da fushinka, ya Ubangiji,Ka kuma tashi ka yi gāba da hasalar abokan gābana!Ka tashi, ka taimake ni, gama adalci kake so a yi.

7. Ka tattaro dukan kabilun da suke kewaye da kai,Ka yi mulki a kansu daga Sama.

8. Ya Ubangiji, kai ne alƙalin dukan mutane.Ka shara'anta mini bisa ga adalcina,Gama ba ni da laifi, ina kuma da kirki.

9. Ka tsai da muguntar mugaye,Ina roƙonka, ka sāka wa mutanen kirki.Kai Allah mai adalci ne,Kana kuwa auna tunanin mutane, da marmarinsu.

10. Allah ne mai kiyaye ni,Yakan ceci waɗanda suke yi masa biyayya.

11. Allah alƙali ne mai adalci,Kullum kuwa yana kā da mugaye.

12. Idan mutane ba su tuba ba,Allah zai wasa takobinsa,

13. Zai ɗana bakansa ya shirya shi,Zai ɗauki makamansa masu dafi,Ya kuma auna kibansa masu wuta.

14. Ka duba, yadda mugu yake tunanin mugunta a ransa,Yana shisshirya wahala, yana kuma aikata ruɗi.

15. Yana haƙa rami mai zurfi a ƙasa,Sa'an nan yă fāɗa ramin da ya haƙa!

16. Saboda haka muguntarsa ta hukunta shi ke nan,Rikicin kansa ya yi masa lahani.

17. Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa,Zan raira yabbai ga Ubangiji, Maɗaukaki.