Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 102 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Wanda Yake Shan Wahala

1. Ka ji addu'ata, ya Ubangiji,Ka ji kukana na neman taimako!

2. Kada ka ɓoye mini sa'ad da nake shan wahala!Ka ji ni, ka amsa mini da sauri sa'ad da na yi kira!

3. Raina ya ɓace kamar hayaƙi,Jikina yana ƙuna kamar wuta.

4. An tattake ni kamar busasshiyar ciyarwa,Ba ni da marmarin cin abinci.

5. Ina nishi da ƙarfi,Ba abin da ya ragu gare ni,In banda ƙashi da fata.

6. Ni kamar tsuntsu nake cikin hamada,Kamar mujiya a kufai.

7. Kwana nake ba barci,Na zama kamar tsuntsun da yake fama da kewaA bisa kan ɗaki.

8. Maƙiyana suna cin mutuncina dukan yini.Waɗanda suke mini ba'a,Suna la'antarwa da sunana.

9. Toka ce abincina,Hawayena kuwa sun gauraya da abin shana,

10. Sabili da fushinka da hasalarka.Ka ɗauke ni, ka jefar da ni.

11. Raina kamar inuwar maraice yake,Kamar busasshiyar ciyawa nake.

12. Amma kai, ya Ubangiji, sarki ne kai har abada,Dukan zamanai masu zuwa za su tuna da kai.

13. Za ka tashi ka ji tausayin Sihiyona,Lokaci ya yi da za ka yi mata jinƙai,Wannan shi ne lokacin!

14. Bayinka suna ƙaunarta,Ko da yake an hallakar da ita,Suna jin tausayinta,Ko da yake ta zama kufai.

15. Sauran al'umma za su ji tsoron Ubangiji,Dukan sarakunan duniya za su ji tsoron ikonsa.

16. Sa'ad da Ubangiji ya sāke gina SihiyonaZai bayyana girmansa.

17. Zai saurari jama'arsa wadda ya rabu da ita,Zai kuwa ji addu'arta.

18. Ku rubuta abin da Ubangiji ya aikata don zamani mai zuwa,Don waɗanda ba a haife su ba tukuna,Su ma su yabe shi.

19. Ubangiji ya duba ƙasaDaga Sama, tsattsarkan wurinsa,Daga Sama ya dubi duniya,

20. Don ya ji nishin ɗaurarru,Don ya saki waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa.

21. Saboda wannan mutane za su yi shelar sunan Ubangiji a Sihiyona,Za su yi masa godiya a Urushalima,

22. Sa'ad da sauran al'umma da mulkoki suka taruDon su yi wa Ubangiji sujada.

23. Tun ina ƙaramin yaro Ubangiji ya sa na rasa ƙarfi,Ya gajerta kwanakina.

24. Ya Allahna, kada ka ɗauke ni a yanzu,Tun da yake ban tsufa ba tukuna!Ya Ubangiji har abada kake.

25. Ka halicci duniya tun tuntuni,Da ikonka ne ka yi sammai.

26. Su za su ɓace duka, amma kai za ka dawwama,Za su ƙare kamar yadda tufafi suke ƙarewa,Za ka sāke su kamar tufafi, za su kuwa ɓace.

27. Amma kai, kana yadda kake kullayaumin,Har abada kake.

28. 'Ya'yanmu za su yi zaman lafiya,Zuriyarsu kuma za su zauna cikin kiyayewarka kullayaumin.