Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 115 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Allah Mai Gaskiya Makaɗaici

1. A gare ka kaɗai, ya Ubangiji,A gare ka kaɗai, ba a gare mu ba,Dole a girmama ka,Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka.

2. Me ya sa sauran al'umma suke tambayarmu,“Ina Allahnku?”

3. Allahnmu yana Sama,Yana aikata yadda yake so.

4. Amma nasu alloli na azurfa da zinariya ne,Da hannu aka siffata su.

5. Suna da baki, amma ba sa magana,Suna da idanu, amma ba sa gani.

6. Suna da kunnuwa, amma ba sa ji,Suna da hanci, amma ba sa jin ƙanshi.

7. Suna da hannuwa, amma ba sa iya riƙon kome,Suna da ƙafafu, amma ba sa iya tafiya.Ba su da murya sam.

8. Ka sa waɗanda suka yi su,Da dukan masu dogara gare su,Su zama kamar gumakan da suka yi!

9. Ku dogara ga Ubangiji, ya ku jama'ar Isra'ila!Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku.

10. Ku dogara ga Ubangiji, ya ku firistoci na Allah!Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku.

11. Ku dogara ga Ubangiji, dukanku waɗanda kuke tsoronsa!Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku.

12. Ubangiji yana tuna da mu, zai kuwa sa mana albarka,Zai sa wa jama'ar Isra'ila albarka,Da dukan firistoci na Allah.

13. Zai sa wa dukan waɗanda suke tsoronsa albarka.Babba da yaro.

14. Ubangiji ya ba ku 'ya'ya,Ku da zuriyarku.

15. Ubangiji, wanda ya yi sama da ƙasaYa sa muku albarka!

16. Samaniya ta Ubangiji ce kaɗai,Amma ya ba mutane duniya.

17. Matacce ba ya yabon Ubangiji,Ko wanda ya gangara zuwa cikin kabari.

18. Amma mu da muke rayayyu, za mu yi masa godiya.A yanzu da har abada.Yabo ya tabbata ga Ubangiji!