Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 147 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Yabon Alherin Allah a kan Urushalima

1. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!Abu mai kyau ne mu yabi Allahnmu,Abu mai daɗi ne, daidai ne kuma, a yabe shi.

2. Ubangiji yana rayar da Urushalima,Yana komo da waɗanda aka kai su baƙunci a wata ƙasa.

3. Yakan warkar da masu karyayyiyar zuciya,Yakan ɗaure raunukansu.

4. Ya ƙididdige yawan taurari,Yakan kira kowanne da sunansa.

5. Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka,Saninsa ya fi gaban aunawa.

6. Yakan ɗaukaka masu tawali'u,Amma yakan ragargaza mugaye har ƙasa.

7. Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji,Ku yabi Allah da garaya.

8. Ya shimfiɗa gajimare a sararin al'arshi.Ya tanada wa duniya ruwan sama,Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai.

9. Yakan ba dabbobi abincinsu,Yakan ciyar da 'ya'yan hankaki sa'ad da suka yi kuka gare shi.

10. Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai,Ba ya murna da jarumawan mayaƙa.

11. Amma yana jin daɗin waɗanda suke tsoronsa,Yana jin daɗin waɗanda suke dogara da madawwamiyar ƙaunarsa.

12. Ya Urushalima, ki yabi Ubangiji,Ya Sihiyona, ki yabi Allahnki.

13. Shi yake riƙe da ƙofofinki da ƙarfi,Yakan sa wa jama'arki albarka.

14. Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya,Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.

15. Yakan ba da umarni,Nan da nan umarnin yakan iso duniya.

16. Yakan aiko da dusar ƙanƙara mai kauri kamar ulu,Ya watsa jaura kamar ƙura.

17. Yakan aiko da ƙanƙara kamar duwatsu,Ba wanda yake iya jurewa da sanyin da yakan aiko!

18. Sa'an nan yakan ba da umarni,Ƙanƙara kuwa ta narke,Yakan aiko da iska, ruwa kuwa yakan gudu.

19. Yana ba Yakubu saƙonsa,Koyarwarsa da dokokinsa kuma ga Isra'ila.

20. Bai yi wa sauran al'umma wannan ba,Domin ba su san dokokinsa ba.Yabo ya tabbata ga Ubangiji!