Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Roƙo da Yabo

1. Ina kira gare ka, ya Ubangiji mai kāre ni,Ka ji kukana!In kuwa ba ka amsa mini ba,Zan zama ɗaya daga cikin waɗanda suka gangara zuwa lahira.

2. Ka ji ni lokacin da na yi kuka gare ka neman taimako,Ina ɗaga hannuwana wajen tsattsarkan Haikalinka.

3. Kada ka kāshe ni tare da mugaye,Tare da masu aikata mugunta,Mutane waɗanda maganarsu kamar ta zumunci ce,Amma zukatansu cike suke da ƙiyayya.

4. Ka hukunta su saboda abin da suka aikata.Ka hukunta su saboda dukan ayyukansu,Ka ba su abin da ya cancance su!

5. Ba su kula da abin da Ubangiji ya yi ba,Ko kuma abin da ya halitta,Don haka zai hukunta su, ya hallaka su har abada.

6. A yabi Ubangiji,Gama ya ji kukana na neman taimako!

7. Ubangiji yakan kiyaye ni, yă tsare ni.Na dogara gare shi.Ya taimake ni, don haka ina murna,Ina raira masa waƙoƙin yabo.

8. Ubangiji yana kiyaye jama'arsa,Yakan kiyaye sarkinsa da ya zaɓa, ya kuma cece shi.

9. Ka ceci jama'arka, ya Ubangiji,Ka sa wa waɗanda suke naka albarka!Ka zama makiyayinsu,Ka lura da su har abada.