Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 103 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Yabon Ƙaunar Allah

1. Ka yabi Ubangiji, ya raina!Ka yabi sunansa mai tsarki!

2. Ka yabi Ubangiji, ya raina,Kada ka manta da yawan alherinsa.

3. Ya gafarta dukan zunubaina,Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena.

4. Ya cece ni daga kabari,Ya sa mini albarka da ƙauna da jinƙai.

5. Ya cika raina da kyawawan abubuwa,Don in zauna gagau,Ƙaƙƙarfa kamar gaggafa.

6. Ubangiji yakan yi wa waɗanda ake zalunta shari'a ta gaskiya.Yakan ba su hakkinsu.

7. Ya faɗa wa Musa shirye-shiryensa.Ya yardar wa jama'ar Isra'ila su ga manyan ayyukansa.

8. Ubangiji mai jinƙai ne, mai ƙauna ne kuma,Mai jinƙirin fushi ne, cike yake da madawwamiyar ƙauna.

9. Ba zai yi ta tsautawa kullum ba,Ba zai yi ta jin haushi har abada ba.

10. Yakan yi mana rangwame sa'ad da yake hukunta mu,Ko sa'ad da yake sāka mana saboda zunubanmu da laifofinmu.

11. Kamar yadda nisan sararin sama yake bisa kan duniya,Haka kuma girman ƙaunarsa yake ga waɗanda suke tsoronsa.

12. Kamar yadda gabas take nesa da yamma,Haka nan ne ya nisantar da zunubanmu daga gare mu.

13. Kamar yadda uba yake yi wa 'ya'yansa alheri,Haka nan kuwa Ubangiji yake yi wa masu tsoronsa alheri.

14. Ubangiji ya san abin da aka yi mu da shi,Yakan tuna, da ƙura aka yi mu.

15. Mutum fa, ransa kamar ciyawa ne,Yakan yi girma, ya yi yabanya kamar furen jeji.

16. Sa'an nan iska ta bi ta kansa, yakan ɓace,Ba mai ƙara ganinsa.

17. Amma ƙaunar Ubangiji ga waɗanda suke girmama shi har abada ce.Alherinsa kuwa tabbatacce ne har dukan zamanai,

18. Ga waɗanda suke riƙe da alkawarinsa da gaskiya,Waɗanda suke biyayya da umarnansa da aminci.

19. Ubangiji ya kafa kursiyinsa a Sama,Shi yake sarautar duka.

20. Ku yabi Ubangiji, ku ƙarfafa, ku manyan mala'iku,Ku da kuke biyayya da umarnansa,Kuna kasa kunne ga maganarsa!

21. Ku yabi Ubangiji, ku dukan ikokin da suke a Sama,Ku yabi Ubangiji, ku bayinsa masu aikata abin da yake so!

22. Ku yabi Ubangiji, dukanku da kuke halittattunsa,A duk inda yake mulki!Ka yabi Ubangiji, ya raina!