Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Kukan Azaba da Waƙar Yabo

1. Ya Allahna, ya Allahna,Don me ka yashe ni?Na yi kuka mai tsanani, ina neman taimako,Amma har yanzu ba ka zo ba!

2. Da rana na yi kira a gare ka, ya Allahna,Amma ba ka amsa ba.Da dare kuma na yi kira,Duk da haka ban sami hutawa ba.

3. Amma an naɗa ka Mai Tsarki,Wanda Isra'ila suke yabonsa.

4. Kakanninmu suka dogara gare ka,Sun dogara gare ka, ka kuwa cece su.

5. Suka yi kira gare ka, suka tsira daga hatsari,Suka dogara gare ka, ba su kuwa kunyata ba.

6. A yanzu dai ni ba mutum ba ne, tsutsa ne kawai,Rainanne, abin ba'a ga kowa da kowa!

7. Duk wanda ya gan niSai yă maishe ni abin dariya,Suna zunɗena da harshensu suna kaɗa kai.

8. Suka ce, “Ka dogara ga Ubangiji,Me ya sa bai cece ka ba?Idan Ubangiji na sonka,Don me bai taimake ka ba?”

9. Kai ne ka fito da ni lafiya a lokacin da aka haife ni,A lokacin da nake jariri ka kiyaye ni.

10. Tun daga lokacin da aka haife ni nake dogara gare ka,Kai ne Allahna tun daga ran da aka haife ni.

11. Kada ka yi nisa da ni!Wahala ta gabato,Ba kuwa mai taimako.

12. Magabta da yawa sun kewaye ni kamar bijimai,Dukansu suna kewaye da ni,Kamar bijimai masu faɗa na ƙasar Bashan.

13. Sun buɗe bakinsu kamar zakoki,Suna ruri, suna ta bina a guje.

14. Ƙarfina ya ƙare,Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa.Dukan gaɓoɓina sun guggulle,Zuciyata ta narke kamar narkakken kakin zuma.

15. Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura,Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama.Ka bar ni matacce cikin ƙura.

16. Ƙungiyar mugaye na kewaye da ni,Suka taso mini kamar garken karnuka,Suka soke hannuwana da ƙafafuna.

17. Ana iya ganin ƙasusuwana duka.Magabtana suka dube ni, suka zura mini ido.

18. Suka rarraba tufafina a tsakaninsu,Suka jefa kuri'a a kan babbar rigata.

19. Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji!Ka gaggauta ka cece ni, ya Mai Cetona!

20. Ka cece ni daga takobi,Ka ceci raina daga waɗannan karnuka.

21. Ka kuɓutar da ni daga waɗancan zakoki,Ba ni da mataimaki a gaban bijimai masu mugun hali.

22. Zan faɗa wa mutanena abin da ka yi,Zan yabe ka cikin taronsu.

23. “Ku yabe shi, ku bayin Ubangiji!Ku girmama shi, ku zuriyar Yakubu!Ku yi masa sujada, ku jama'ar Isra'ila!

24. Ba ya ƙyale matalauta,Ko ya ƙi kulawa da wahalarsu,Ba ya rabuwa da su,Amma yakan amsa lokacin da suka nemi taimako.”

25. Zan yabe ka a gaban babban taron jama'aSaboda abin da ka yi,A gaban dukan masu yi maka biyayya,Zan miƙa sadakokin da na alkawarta.

26. Matalauta za su ci yadda suke so,Masu zuwa wurin Ubangiji za su yabe shi,Su arzuta har abada!

27. Dukan al'ummai za su tuna da Ubangiji,Za su zo gare shi daga ko'ina a duniya,Dukan kabilai za su yi masa sujada.

28. Ubangiji Sarki ne,Yana mulki a kan al'ummai.

29. Masu girmankai duka za su rusuna masa,'Yan adam duka za su rusuna masa,Dukan waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa.

30. Zuriya masu zuwa za su bauta masa,Mutane za su ambaci Ubangiji ga zuriya mai zuwa.

31. Mutanen da ba a haifa ba tukuna, za a faɗa musu,“Ubangiji ya ceci jama'arsa!”