Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Neman Tsari daga Mugaye

1. Ka kasa kunne ga kalmomina, ya Ubangiji,Ka kuma ji ajiyar zuciyata.

2. Ya Sarkina, Allahna,Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako.

3. A gare ka zan yi addu'a, ya Ubangiji,Da safe za ka ji muryata,Da hantsi zan yi addu'ata,In kuma jira amsa.

4. Kai ba Allah mai yarda da aikin kuskure ba ne,Ba ka yarda da mugunta a gabanka.

5. Ba ka jurewa da ganin mutane masu fāriya,Kana ƙin mugaye.

6. Kakan hallakar da duk maƙaryata,Kakan raina masu ta da hankali da masu ruɗi.

7. Amma ni, ina iya zuwa wurinka,Saboda ƙaunarka mai girma,In yi sujada a tsattsarkan Haikalinka,In kuma rusuna maka da bangirma.

8. Ina da abokan gāba da yawa, ya Ubangiji,Ka bi da ni in aikata nufinka,Ka kuma fayyace mini hanyarka domin in bi ta!

9. Abin da maƙiyana ke faɗa,Ba abin da za a yarda da shi ba ne,Su dai, so suke su hallakar kawai,Bakinsu kamar buɗaɗɗen kabari yake,Maganganunsu kuwa suna da taushi da kuma yaudara.

10. Ka kāshe su, ka hukunta su, ya AllahKa watsar da mugayen shirye-shiryensu,Ka kore su daga gabanka sabili da yawan zunubansu,Da kuma tayarwar da suke yi maka.

11. Duk waɗanda suka fake gare ka za su yi farin ciki,Kullum za su yi ta raira waƙa domin murna.Kana kiyaye waɗanda suke ƙaunarka,Suna kuwa matuƙar murna saboda kai.

12. Ka sa wa masu yi maka biyayya albarka, ya Ubangiji,Alherinka yana kāre su kamar gārkuwa.