Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 135 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Waƙar Yabon Girman Ubangiji

1. Ku yabi Ubangiji!Ku yabi sunansa, ku bayin Ubangiji,

2. Ku da kuke tsaye a Haikalin Ubangiji,A wuri mai tsarki na Allahnmu.

3. Ku yabi Ubangiji, domin nagari ne shi,Ku raira yabbai ga sunansa, domin shi mai alheri ne.

4. Ya zaɓar wa kansa Yakubu,Jama'ar Isra'ila kuwa tasa ce.

5. Na sani Ubangijinmu mai girma ne,Ya fi dukan alloli girma.

6. Yana aikata dukan abin da ya ga dama a Sama ko a duniya,A tekuna, da kuma zurfafan da suke ƙarƙas.

7. Yakan kawo gizagizan hadiri daga bangayen duniya,Yakan yi walƙiya domin hadura,Yakan fito da iska daga cikin taskarsa.

8. A Masar ne ya karkashe 'ya'yan fari na mutane da na dabbobi.

9. A can ne ya aikata mu'ujizai da al'ajabai,Domin ya hukunta Fir'auna da dukan hukumar ƙasarsa.

10. Ya hallakar da sauran al'umma masu yawa,Ya karkashe sarakuna masu iko, wato

11. Sihon, Sarkin Amoriyawa, da Og, Sarkin Bashan,Da dukan sarakunan Kan'ana.

12. Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa,Ya ba da ita ga Isra'ila.

13. Ya Ubangiji, kullayaumi mutane za su sani kai ne Allah,Dukan tsararraki za su tuna da kai.

14. Ubangiji zai ji juyayin mutanensa,Zai 'yantar da bayinsa.

15. Gumakan al'ummai, da azurfa da zinariya aka yi su,Hannuwan mutane ne suka siffata su.

16. Suna da bakuna, amma ba sa magana,Da idanu, amma ba sa gani.

17. Suna da kunnuwa, amma ba sa ji,Ba kuma numfashi a bakinsu.

18. Ka sa su waɗanda suka yi su,Da dukan waɗanda suke dogara gare su,Su zama kamar gumakan da suka yi!

19. Ku yabi Ubangiji, ya jama'ar Isra'ila,Ku yabe shi, ya ku firistocin Allah!

20. Ku yabi Ubangiji, ya ku Lawiyawa,Ku yabe shi, dukanku da kuke tsoronsa!

21. Ku yabi Ubangiji a Sihiyona da a Urushalima, wato a Haikalinsa.Ku yabi Ubangiji!