Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 39 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Rai Mai Halin Shuɗewa

1. Na ce, “Zan yi hankali da abin da nake yi,Don kada harshena yă sa ni zunubi,Ba zan ce kome ba sa'ad da mugaye suke kusa.”

2. Na yi shiru, ban ce kome ba,Ko a kan abin da suke da kyau!Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi,

3. Zuciyata kuwa ta cika da taraddadi,Bisa ga yawan tunanina, haka yawan wahalata zai zama,Dole ne in yi ta tambaya,

4. “Ya Ubangiji, kwana nawa zan yi a duniya?Yaushe zan mutu?Ka koya mini ranar da ajalina zai auko.

5. “Ga shi, ka gajerta yawan kwanakina!Yawan kwanakina a wurinka kamar ba kome ba ne.Hakika duk mutum mai rai,Bai fi shaƙar iska ba.

6. Bai kuma fi inuwa ba!Duk abin da yake yi banza ne,Yakan tara dukiya, amma bai san wanda zai more ta ba!

7. “A kan me zan sa zuciya, ya Ubangiji?A gare ka nake dogara.

8. Ka cece ni daga dukan zunubaina,Kada ka bar wawaye su yi mini ba'a.

9. Zan yi shiru, ba zan ce kome ba,Saboda ka sa na sha wahala haka.

10. Kada ka ƙara hukunta ni!Na kusa mutuwa saboda bugun da kake yi mini!

11. Kakan hukunta zunuban mutum ta wurin tsautawarka,Kamar yadda asu yake lalata abu.Hakika mutum bai fi shaƙar iska ba!

12. “Ka ji addu'ata, ya Ubangiji,Ka kuma kasa kunne ga roƙona,Kada ka yi shiru sa'ad da na yi kuka gare ka!Yadda dukan kakannina suka yi,Ni baƙonka ne na ɗan lokaci.

13. Ka ƙyale ni ko zan sami kwanciyar rai,Kafin in tafi, ai, tawa ta ƙāre.”