Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Mai Shan Wuya

1. Kada ka yi fushi har ka tsauta mini, ya Ubangiji!Kada ka hukunta ni da fushinka!

2. Ka hukunta ni, ka kuwa yi mini rauni,Ka kuma buge ni har ƙasa.

3. Saboda fushinka ina ciwo mai tsanani,Duk jikina ya kamu da ciwo saboda zunubina.

4. Ina nutsewa cikin ambaliyar zunubaina,Ina jin nauyinsu, sun danne ni ƙasa.

5. Saboda wawancina, miyakuna sun ruɓe, suna wari,

6. An tanƙware ni, an ragargaza ni,Ina ta kuka dukan yini.

7. Ina fama da zazzaɓi,Ina rashin lafiya ƙwarai.

8. An ragargaza ni sarai, an kuwa ci nasara a kaina,Na damu a zuciyata, ina nishi don zafi.

9. Ka san bukatata, ya Ubangiji,Kana jin dukan nishe-nishena.

10. Zuciyata tana ɗar, ƙarfina ya ƙāre,Idanuna sun dushe.

11. Abokaina da maƙwabtana ba su ko zuwa kusa da ni, saboda miyakuna,Har iyalina ma sun guje mini.

12. Masu son kashe ni, sun haƙa mini tarkuna,Masu so su cuce ni, suna barazanar lalatar da ni,Yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.

13. Kamar kurma nake, ba na iya ji,Kamar kuma bebe, ba na iya magana.

14. Ni kamar mutumin da ba ya iya amsawa nake, don ba na ji.

15. Na dogara gare ka, ya Ubangiji,Kai za ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna.

16. Kada ka bar magabtana su yi murna saboda wahalata.Kada ka bar su su yi kirari a kan faɗuwata!

17. Ina gab da fāɗuwa,Ina cikin azaba kullum.

18. Na hurta zunubaina,Sun cika ni da taraddadi.

19. Magabtana lafiyayyu ne masu ƙarfi.Waɗanda yake ƙina ba dalili, suna da yawa.

20. Masu rama nagarta da mugunta,Suna gāba da ni,Domin ina ƙoƙarin aikata abin da yake daidai.

21. Kada ka yashe ni, ya Ubangiji,Kada ka rabu da ni, ya Allahna!

22. Sai ka taimake ni yanzu, ya Ubangiji, Mai Cetona!