Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 77 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Ta'aziyya a Lokacin Damuwa

1. Na ta da murya, na yi kuka ga Allah,Na ta da murya, na yi kuka, ya kuwa ji ni.

2. A lokacin wahala, nakan yi addu'a ga Ubangiji,Dukan dare nakan ɗaga hannuwana sama in yi addu'a,Amma ban sami ta'aziyya ba.

3. Lokacin da na tuna da Allah na yi ajiyar zuciya.Sa'ad da nake tunani,Nakan ji kamar in fid da zuciya.

4. Ba ya barina in yi barci,Na damu har na kāsa magana.

5. Na yi tunanin kwanakin da suka wuce,Nakan kuma tuna da shekarun da suka wuce da daɗewa.

6. Dare farai ina ta tunani mai zurfi,A cikin tunani nakan yi wa kaina tambaya.

7. A kullum ne Ubangiji zai yashe ni?Ba kuma zai ƙara yin murna da ni ba?

8. Ya daina ƙaunata ke nan?Alkawarinsa ba shi da wani amfani?

9. Allah ya manta da yin jinƙai ne?Fushinsa ya maye matsayin juyayinsa ne?

10. Sa'an nan sai na ce, “Abin da ya fi mini zafi duka,Shi ne ikon Maɗaukaki ya ragu.”

11. Zan tuna da manyan ayyukanka, ya Ubangiji,Zan tuna da al'amura masu banmamaki da ka aikata a dā.

12. Zan tuna da dukan abubuwan da ka yi,Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka.

13. Dukan abin da kake yi mai tsarki ne, ya Allah!Ba wani allah mai girma kamarka!

14. Kai ne Allah wanda kake aikata al'ajabai,Ka nuna ikonka cikin sauran al'umma.

15. Ta wurin ikonka ka fanshi jama'arka,Zuriyar Yakubu da ta Yusufu.

16. Ya Allah, sa'ad da ruwaye suka gan ka, sai su tsorata,Zurfafan teku kuma suka yi rawar jiki.

17. Gizagizai suka zubo da ruwa,Aka buga tsawa daga sama,Aka kuwa yi walƙiya ko'ina.

18. Bugawar tsawarka ta gama ko'ina,Hasken walƙiya ya haskaka dukan duniya,Duniya ta yi rawa, ta girgiza, ta kaɗu.

19. Ka yi tafiya a teku,Ka haye teku mai zurfi,Amma ba a ga shaida inda ka taka ba.

20. Ka bi da jama'arka yadda makiyayi yake yi,Musa da Haruna suke lura da su.