Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 50 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Allah ne Mai Shari'a

1. Allah Maɗaukaki, Ubangiji, ya yi magana,Yana kiran dukan duniya, daga gabas zuwa yamma.

2. Allah yana haskakawa daga Sihiyona,Da cikar jamalin Sihiyona.

3. Allahnmu ya zo, ba a ɓoye yake ba,Wuta mai cinyewa na tafe a gabansa,Babban hadiri kuwa na kewaye da shi.

4. Ya kira sammai da duniya su zama shaidu,Su ga yadda yake shara'anta jama'arsa.

5. Ya ce, “Ku tattaro mini amintattuna,Waɗanda suka cika alkawarin da yake tsakanina da su,Ta wurin miƙa hadaya.”

6. Sammai suna shelar adalcin Allah,Domin shi yake yin shari'a!

7. “Ku ji, ya ku jama'ata, zan kuwa yi magana,Zan ba da shaida gāba da ku, ya Isra'ila.Ni ne Allah, Allahnku.

8. Ban tsauta muku saboda hadayunku ba,Ko saboda hadayu na ƙonawa da kuke ta miƙa mini kullum.

9. Ba na bukatar bijimai daga gonakinku,Ko awaki daga garkunanku.

10. Gama namomin jeji nawa ne,Dubban shanu da suke kan tuddai kuma nawa ne.

11. Dukan tsuntsayen da suke tashi a sararin sama nawa ne,Da dukan masu rai da suke ƙasa.

12. “Da ina jin yunwa ba sai na faɗa muku ba,Gama da duniya da dukan abin da yake cikinta nawa ne.

13. Nakan ci naman bijimai ne?Ko nakan sha jinin awaki?

14. Bari ku miƙa wa Allah hadayarku ta godiya,Ku ba Mai Iko Dukka, dukan hadayun da kuka alkawarta.

15. Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo,Zan cece ku,Ku kuwa za ku yabe ni.”

16. Amma Allah ya ce wa mugaye,“Don me za ku haddace umarnaina?Don me za ku yi magana a kan alkawaraina?

17. Kun ƙi in tsauta muku,Kun yi watsi da umarnaina.

18. Sa'ad da kuka ga ɓarawo kukan yi abuta da shi.Kuna haɗa kai da mazinata.

19. “Kullum a shirye kuke ku hurta mugunta,Ba ku jin nauyin faɗar ƙarya.

20. A shirye kuke ku sari 'yan'uwanku,Ku sa musu laifi.

21. Kun aikata waɗannan duka, ni kuwa ban ce kome ba,Saboda haka kuka zaci ni kamar ku nake.Amma yanzu zan tsauta muku,In bayyana muku al'amarin a fili.

22. “Ku ji wannan ku da kuke ƙyale ni,In ba haka ba zan hallaka ku,Ba wanda zai cece ku.

23. Wanda yake yin godiya a sa'ad da yake miƙa hadayarsa, yana girmama ni,Da wanda yake yi mini biyayya kuma, zan nuna masa cetona.”