Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 76 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Allah Mai Nasara Mai Hukunci

1. Allah sananne ne a Yahuza,Mashahuri ne kuma a Isra'ila.

2. Wurin zamansa yana Urushalima,A dutsen Sihiyona zatinsa yake.

3. A can yake kakkarya kiban abokan gāba,Da garkuwoyinsu, da takubansu, i, har da dukan makamansu.

4. Ina misalin darajarka, ya Allah!Ina misalin ɗaukakarka a sa'ad da ka komo daga kan duwatsu,Daga korar abokan gābanka!

5. An kwashe ganimar sojojinsu masu ƙarfin hali,Yanzu suna barci, barcin matattu,Ba waninsu da ya ragu,Da zai yi amfani da makamansa.

6. Sa'ad da ka fafare su, ya Allah na Yakubu,Dawakansu da mahayansu suka fāɗi matattu.

7. Amma mutane suna jin tsoronka!Wa zai iya tsayawa a gabankaSa'ad da ka yi fushi?

8. Daga Sama ka sanar da shari'arka,Duniya ta tsorata, ta yi tsit,

9. Sa'ad da ka tashi domin ka yanke hukunci,Domin ka ceci waɗanda ake zalunta a duniya.

10. Hasalar mutane ba ta ƙara kome, sai dai ta ƙara maka yabo.Waɗanda suka tsira daga yaƙe-yaƙe za su kiyaye idodinka.

11. Ku ba Ubangiji Allahnku abin da kuka alkawarta masa,Dukanku sauran al'umma da kuke kusa, ku kawo masa kyautai.Allah yakan sa mutane su ji tsoronsa,

12. Yakan ƙasƙantar da shugabanni masu girmankai,Ya tsoratar da manyan sarakuna.