Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 139 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Cikakken Sanin Allah da Kulawarsa

1. Ya Ubangiji, ka jarraba ni, ka san ni.

2. Ka sa dukan abin da nake yi,Tun daga can nesa ka gane dukan tunanina.

3. Kana ganina, ko ina aiki, ko ina hutawa,Ka san dukan ayyukana.

4. Tun kafin in yi maganaKa riga ka san abin da zan faɗa.

5. Kana kewaye da ni a kowane sashe,Ka kiyaye ni da ikonka.

6. Yadda ka san ni ya fi ƙarfin magana,Ya yi mini zurfi, ya fi ƙarfin ganewata.

7. Ina zan tafi in tsere wa Ruhunka?Ina zan gudu in tsere maka?

8. Idan na hau cikin samaniya kana can,In na kwanta a lahira kana can,

9. In na tashi sama, na tafi, na wuce gabas,Ko kuma na zauna a can yamma da nisa,

10. Kana can domin ka bi da ni,Kana can domin ka taimake ni.

11. Da na iya roƙon duhu ya ɓoye ni,Ko haske da yake kewaye da niYa zama dare,

12. Amma har duhun ma, ba duhu ba ne a gare ka,Dare kuwa haskensa kamar na rana ne.Duhu da haske, duk ɗaya ne gare ka.

13. Kai ne ka halicci kowace gaɓa ta jikina,Kai ne ka harhaɗa ni a cikin mahaifiyata.

14. Ina yabonka gama kai abin tsoro ne,Dukan abin da ka yi sabo ne, mai banmamaki.Da zuciya ɗaya na san haka ne.

15. Ka ga lokacin da ƙasusuwana suke siffatuwa,Sa'ad da kuma ake harhaɗa su a hankaliA cikin mahaifiyata,Lokacin da nake girma a asirce.

16. Ka gan ni kafin a haife ni.Ka ƙididdige kwanakin da ka ƙaddara mini,Duka an rubuta su a littafinka,Tun kafin faruwar kowannensu.

17. Ya Allah, tunaninka suna da wuyar ganewa a gare ni,Ba su da iyaka!

18. In na ƙirga su, za su fi tsabar yashi,Sa'ad da na farka, har yanzu ina tare da kai.

19. Ya Allah, da yadda nake so ne, da sai ka karkashe mugaye!'Yan ta da zaune tsaye kuma sai su rabu da ni!

20. Suna ambaton mugayen abubuwa a kanka,Suna faɗar mugayen abubuwa gāba da sunanka.

21. Ya Ubangiji, ga yadda nake ƙin waɗanda suke ƙinka,Da yadda nake raina waɗanda suke tayar maka!

22. Ƙiyayyar da nake yi musu ta kai intaha,Na ɗauke su, su abokan gābana ne.

23. Jarraba ni, ya Allah, ka san tunanina,Gwada ni, ka gane damuwata.

24. Ka bincike, ko akwai wani rashin gaskiya a gare ni,Ka bi da ni a madawwamiyar hanya.