Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 90 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Allah Madawwami, Mutum mai Shuɗewa

1. Ya Ubangiji, a koyaushe kai ne wurin zamanmu.

2. Kafin a kafa tuddai,Kafin kuma ka sa duniya ta kasance,Kai Allah ne, Madawwami.Ba ka da farko, ba ka da ƙarshe.

3. Kakan sa mutane su koma yadda suke,Su zama ƙura.

4. A gare ka shekara dubu, kamar kwana ɗaya ne,Kamar jiya ce wadda ta shige,Gajeruwa ce kamar sa'a guda ta dare.

5. Kakan kwashe mutane kamar yadda ambaliyar ruwa take yi,Kamar mafarki suke, ba su daɗewa.Kamar tsire-tsire suke waɗanda suke tsirowa da safe,

6. Su yi girma har su yi huda,Sa'an nan su yi yaushi su bushe da yamma.

7. Mun halaka ta wurin fushinka,Mun razana saboda hasalarka.

8. Ka jera zunubanmu a gabanka,Zunubanmu na ɓoye kuwa,Ka sa su a inda za ka gan su.

9. Fushinka ya gajerta tsawon ranmu,Ranmu ya ƙare kamar ajiyar zuciya.

10. Tsawon kwanakin ranmu duka a ƙalla shekara ce saba'in,In kuwa muna da ƙarfi, shekara tamanin ne.Duk da haka iyakar abin da waɗannan shekaruSuke kawo mana, damuwa ce da wahala,Nan da nan sukan wuce,Tamu da ƙare.

11. Wa ya san iyakar ikon fushinka?Wa ya san irin tsoron da hasalarka za ta kawo?

12. Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne,Domin mu zama masu hikima.

13. Ya Ubangiji, sai yaushe za ka ji tausayinmu?Ka ji tausayin bayinka!

14. Ka cika mu da madawwamiyar ƙaunarka a kowace safiya,Don mu raira waƙoƙin murna dukan kwanakin ranmu.

15. Yanzu sai ka sa mu yi farin ciki mai yawa,Kamar yadda ka sa muka yi baƙin cikiA dukan shekarun nan, da muka sha wahala.

16. Ka yarda mana, mu bayinka, mu ga ayyukanka masu girma,Ka yardar wa zuriyarmu su ga ikonka mai girma.

17. Ka yarda, albarkarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji Allahnmu.Ka sa mu yi nasara game da dukan abin da za mu yi!I, ka ba mu nasara a dukan abin da muke yi!