Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 73 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Ƙarshen Mugaye

1. Hakika, Allah yana yi wa Isra'ila alheri,Da waɗanda suke da tsarkin zuciya!

2. Amma ina gab da fāɗuwa,Ƙafafuna sun kusa zamewa,

3. Saboda na ji kishin masu girmankai,Sa'ad da na ga mugaye suna arziki.

4. Ba su jin zafin ciwo,Su ƙarfafa ne, lafiyayyu.

5. Ba su shan wahala yadda sauran mutane suke sha,Ba su da wahala kamar sauran mutane,

6. Don haka suka ɗaura girmankai kamar dutsen wuya,Suka sa hargitsi kuma kamar riga.

7. Zuciyarsu, cike take da mugunta,Tunaninsu kuma cike suke da mugayen ƙulle-ƙulle.

8. Sukan yi wa waɗansu ba'a,Suna faɗar mugayen abubuwa,Masu girmankai ne su, suna shawaraA kan yadda za su zalunci waɗansu.

9. Sukan faɗi baƙar magana a kan Allah na Sama,Su ba da umarnai na girmankai ga mutane a duniya,

10. Har jama'ar Allah ma sukan koma wurinsu,Suna ɗokin gaskata dukan abin da suke faɗa musu.

11. Sukan ce, “Ai, Allah ba zai sani ba,Maɗaukaki ba zai bincika ba!”

12. Haka mugaye suke.Suna da dukiya da yawa, amma sai ƙaruwa suke ta yi.

13. Ashe, a banza nake kiyaye kaina da tsarki,Hannuwana kuma a tsabtace daga zunubi?

14. Ya Allah, ka sa ina shan wahala dukan yini,Kana horona kowace safiya!

15. Da na faɗi waɗannan abubuwa,Da na zama marar gaskiya ga jama'arka.

16. Don haka na yi iyakar ƙoƙari in fahimci wannan,Ko da yake ya cika wuya,

17. Sai sa'ad da na shiga Haikalinka,Sa'an nan na fahimci abin da zai sami mugaye.

18. Hakika ka sa su a wurare masu santsi,Ka sa su su fāɗi su hallaka sarai!

19. Cikin ƙyaftawar ido aka hallaka su,Suka yi mummunan ƙarshe!

20. Ya Ubangiji, kamar mafarki sukeWanda akan manta da shi da safe,Sa'ad da mutum ya farka yakan manta da kamanninsa.

21. Sa'ad da zuciyata ta ɓaci,Hankalina ya tashi,

22. Sai na zama wawa, ban fahimta ba,Na nuna halin dabba a gabanka.

23. Duk da haka ina tare da kai kullayaumin,Kana riƙe da hannuna.

24. Shawararka, tana bi da ni,Daga ƙarshe kuma za ka karɓe ni da daraja.

25. In banda kai, wa nake da shi a Sama?Tun da yake ina da kai, me kuwa nake bukata a duniya?

26. Kwanyata da jikina za su raunana,Amma Allah ne ƙarfina,Shi nake so har abada!

27. Hakika waɗanda za su rabu da kai za su mutu,Za ka hallakar da marasa aminci gare ka.

28. Amma a gare ni, ya fi mini kyau, in kasance kusa da Allah!Na sami mafaka a wurin Ubangiji Allah,Da zan yi shelar dukan abin da ya aikata.