Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Godiya ga Allah saboda Adalcinsa

1. Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji,Zan hurta dukan abubuwa masu banmamaki da ka yi.

2. Zan raira waƙa da farin ciki sabili da kai,Zan raira yabo gare ka, ya Maɗaukaki!

3. Magabtana sun jā da baya da suka gan ka,Suka faɗi, suka mutu.

4. Kai da kake alƙali mai adalciKa zauna a kursiyinka,Ka kuwa yi shari'ar da ta yi mini daidai.

5. Ka kā da arna,Ka kuma hallakar da mugaye,Ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba.

6. An hallaka abokan gābanmu har abada,Ka lalatar da biranensu,An kuma manta da su sarai.

7. Amma Ubangiji sarki ne har abada,Ya kafa kursiyinsa domin yin shari'a.

8. Yana mulkin duniya da adalci,Yana yi wa mutane shari'a da gaskiya.

9. Ubangiji mafaka ne ga waɗanda ake zalunta,Wurin ɓuya a lokatan wahala.

10. Waɗanda suka san ka za su amince da kai, ya Ubangiji,Ba za ka ƙyale duk wanda ya zo gare ka ba.

11. Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona!Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi!

12. Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya,Ba ya mantawa da kukansu,Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu.

13. Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai!Ka dubi irin wulakancin da maƙiya suka yi mini!Ka kuɓutar da ni daga mutuwa, ya Ubangiji,

14. Domin in iya tsayawa a gaban jama'ar Urushalima,In faɗa musu dukan abin da ya sa nake yabonka.Zan yi farin ciki saboda ka cece ni.

15. Arna sun haƙa rami sun kuwa fāɗa ciki,Sun ɗana tarko, ya kuwa kama su.

16. Ubangiji ya bayyana kansa ta wurin shari'arsa mai adalci,Mugaye sun kama kansu da abubuwan da suka aikata.

17. Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye,Da dukan waɗanda suke ƙin Allah.

18. Ba kullum ne ake ƙyale masu bukata ba,Ba za a danne sa zuciyar waɗanda ake zalunta ba har abada.

19. Ka zo, ya Ubangiji! Kada ka bari mutane su gagare ka!Ka kawo arna a gabanka, ka hukunta su.

20. Ka sa su ji tsoro, ya Ubangiji,Ka sa su sani su mutane ne kawai.