Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 91 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Zama a Inuwar Mai Iko Dukka

1. Duk wanda ya je wurin MaɗaukakiZai zauna lafiya,Duk wanda yake zaune a inuwar Mai Iko Dukka,

2. Ya iya ce wa Ubangiji,“Kai ne kāriyata, da mai kiyaye ni!Kai ne Allahna, a gare ka nake dogara!”

3. Hakika zai kiyaye kaDaga dukan hatsarorin da ka ɓoye,Daga kuma dukan mugayen cuce-cuce.

4. Zai rufe ka da fikafikansa,Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu.Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka.

5. Ba za ka ji tsoron hatsarori da dare ba,Ko fāɗawar da za a yi maka da rana,

6. Ko annobar da take aukowa da dare,Ko mugayen da suke kisa da tsakar rana.

7. Mutum dubu za su fāɗi daura da kai,Dubu goma kuma za su fāɗi dama da kai,Amma kai, ba za a cuce ka ba.

8. Da idonka za ka duba, Ka ga yadda ake hukunta wa mugaye.

9. Domin ka ɗauka Ubangiji yake kiyaye ka,Maɗaukaki ne yake tsaronka,

10. To, ba bala'in da zai same ka,Ba za a yi wa gidanka aikin ƙarfi da yaji ba.

11. Allah zai sa mala'ikunsa su lura da kai,Za su kiyaye ka duk inda za ka tafi.

12. Za su ɗauke ka a hannuwansu,Don kada ka buga ƙafarka a dutse.

13. Za ka tattake zakoki da macizai,Za ka tattake zakoki masu zafin raiDa macizai masu dafi.

14. Allah ya ce, “Zan ceci waɗanda suke ƙaunata,Zan kiyaye waɗanda suka san ni.

15. Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu,Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala,Zan cece su in girmama su.

16. Zan ba su tsawon rai lada,Hakika kuwa zan cece su.”