Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Neman Tsari daga Azzalumai

1. Ka kasa kunne ga roƙona, ni adalin mutum,Ka lura da kukana na neman taimako!Ka kasa kunne ga addu'ata,Gama ni ba mayaudari ba ne.

2. Za ka shara'anta shari'ar da za ta gamshe ni,Saboda ka san abin da yake daidai.

3. Ka san zuciyata,Kakan zo gare ni da dare,Ka riga ka jarraba ni sarai,Ba ka kuwa sami mugun nufi a cikina ba.Na ƙudurta kuma bakina ba zai yi saɓo ba.

4. Zancen aikin sauran mutane,Na yi biyayya ga umarninkaBan bi hanyar rashin hankali ba.

5. Ina tafiya a kan tafarkinka kullum,Ban kuwa kauce ba.

6. Ina addu'a gare ka, ya Allah,Domin kakan amsa mini,Don haka ka juyo wurina ka kasa kunne ga maganata.

7. Ka bayyana ƙaunarka mai banmamaki,Ya Mai Ceto,Muddin muna kusa da kai mun tsira daga maƙiyanmu.

8. Ka kiyaye ni kamar yadda ake kiyaye idanu,Ka ɓoye ni a inuwar fikafikanka,

9. Daga hare-hare na mugaye.Maƙiyana cike da ƙiyayya sun kewaye ni.

10. Ba su jin tausayi, suna magana da girmankai,

11. Yanzu suna kewaye da ni duk inda na juya,Suna jira su sami dama su fyaɗa ni ƙasa.

12. Kamar zakoki suke nema su yayyage ni kaca-kaca,Kamar sagarun zakoki suna fakona a wurin ɓuyarsu.

13. Ka zo, ya Ubangiji,Ka yi yaƙi da maƙiyana, ka yi nasara da su!Ka cece ni da takobinka daga mugaye,

14. Ka cece ni daga gare su da ikonka,Ka cece ni daga waɗanda suke da duk abin da suke so a duniyan nan,Ka hukunta su da wahalar da ka shirya musu,Ka sa har 'ya'yansu, su ma, ta ishe su,Wahalar da ta ragu kuma, ta sami jikokinsu!

15. Zan gan ka domin ni adali ne,Sa'ad da na farka, kasancewarka tana cika ni da farin ciki.