Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 59 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Neman Ceto daga Maƙiya

1. Ka cece ni daga maƙiyana, ya Allahna,Ka kiyaye ni daga waɗanda suka tasar mini!

2. Ka cece ni daga waɗannan mugaye,Ka tsirar da ni daga masu kisankan nan!

3. Duba! Suna jira su auka mini,Mugaye suna taruwa gāba da ni,Ba domin wani zunubi ko wani laifin da na yi ba,

4. Ba domin na yi wani laifi ba, ya Ubangiji,Har da suka gaggauta gāba da ni.Kai da kanka ka gani, ya Allah na Isra'ila!Ka tashi ka taimake ni.

5. Ka tashi, ya Ubangiji, Allah Maɗaukaki, ka taimake ni,Ka tashi ka hukunta al'ummai,Kada ka yi wa waɗannan mugaye, maciya amana, jinƙai!

6. Da maraice suka komo,Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni.

7. Ji abin da suke fada!Harsunansu suna kama da takuba a bakinsu,Duk da haka suna ta tambaya, suna cewa, “Wa zai ji mu?”

8. Amma kai dariya kake yi musu, ya Ubangiji,Ka mai da al'ummai duka abin bandariya!

9. Mai tsarona, kai ne kake kiyaye ni,Kai ne mafakata, ya Allah.

10. Allahna wanda yake ƙaunata, zai zo gare ni,Zai sa in ga an kori magabtana.

11. Kada ka kashe su, ya Allah, don kada jama'ata su manta.Ka watsar da su da ikonka, ka hallaka su ya Ubangiji mai kiyaye mu!

12. Zunubi na cikin leɓunansu, maganganunsu na zunubi ne,Da ma a kama su saboda girmankansu,Domin suna la'antarwa, suna ƙarya!

13. Da fushinka ka hallaka su,Ka hallaka su ɗungum.Sa'an nan jama'a za su sani Allah yana mulkin Isra'ila,Mulkinsa ya kai ko'ina a duniya!

14. Da maraice maƙiyana suka komo,Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni.

15. Suna kai da kawowa ko'ina neman abinci,In ba su sami abin da ya ishe su ba,Sukan yi gunaguni.

16. Amma zan raira waƙa a kan ikonka,Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfiGa zancen madawwamiyar ƙaunarka.Kai mafaka ne a gare ni,Wurin ɓuya a kwanakin wahala.

17. Zan yabe ka, mai tsarona,Allah ne mafakata,Allah wanda ya ƙaunace ni.