Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 75 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Allah Ya Ƙasƙantar da Mugaye, Ya Ɗaukaka Adalai

1. Muna yabonka, ya Allah, muna yabonka!Muna shelar sunanka mai girma,Muna kuwa faɗa abubuwan banmamaki da ka aikata!

2. “Na ƙayyade lokacin yin shari'a,” in ji Ubangiji Allah,“Zan kuwa yi shari'ar gaskiya.

3. Ko da duniya da dukan waɗanda yake zaune cikinta za su ɓace,Zan ƙarfafa harsashin gininta.

4. Na faɗa wa masu girmankai kada su yi taƙama,Na kuma faɗa wa mugaye kada su yi fāriya,

5. Na dai faɗa musu su daina yanga,Su daina yin taƙama.”

6. Hukunci ba daga gabas, ko yamma,Ko daga kudu, ko arewa yake zuwa ba.

7. Allah yake yin shari'a,Yana ƙasƙantar da waɗansu, ya kuma ɗaukaka waɗansu.

8. Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo,Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi,Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha,Suka shanye shi ƙaƙaf.

9. Amma har abada ba zan daina yin magana a kan Allah na Yakubu ba,Ko in daina raira yabbai gare shi.

10. Shi zai karya ikon mugaye,Amma za a ƙara wa masu adalci ƙarfi.