Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52
  53. 53
  54. 54
  55. 55
  56. 56
  57. 57
  58. 58
  59. 59
  60. 60
  61. 61
  62. 62
  63. 63
  64. 64
  65. 65
  66. 66
  67. 67
  68. 68
  69. 69
  70. 70
  71. 71
  72. 72
  73. 73
  74. 74
  75. 75
  76. 76
  77. 77
  78. 78
  79. 79
  80. 80
  81. 81
  82. 82
  83. 83
  84. 84
  85. 85
  86. 86
  87. 87
  88. 88
  89. 89
  90. 90
  91. 91
  92. 92
  93. 93
  94. 94
  95. 95
  96. 96
  97. 97
  98. 98
  99. 99
  100. 100
  101. 101
  102. 102
  103. 103
  104. 104
  105. 105
  106. 106
  107. 107
  108. 108
  109. 109
  110. 110
  111. 111
  112. 112
  113. 113
  114. 114
  115. 115
  116. 116
  117. 117
  118. 118
  119. 119
  120. 120
  121. 121
  122. 122
  123. 123
  124. 124
  125. 125
  126. 126
  127. 127
  128. 128
  129. 129
  130. 130
  131. 131
  132. 132
  133. 133
  134. 134
  135. 135
  136. 136
  137. 137
  138. 138
  139. 139
  140. 140
  141. 141
  142. 142
  143. 143
  144. 144
  145. 145
  146. 146
  147. 147
  148. 148
  149. 149
  150. 150

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Zab 86 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Addu'ar Neman Jinƙan Allah

1. Ka kasa kunne gare ni, ya Ubangiji, ka amsa mini,Gama ba ni da ƙarfi, ba ni kuwa da mataimaki.

2. Ka cece ni daga mutuwa, saboda ni mai aminci ne a gare ka,Ka cece ni saboda ni bawanka ne, ina kuwa dogara gare ka.

3. Kai ne Allahna, saboda haka ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji,Ina yin addu'a a gare ka dukan yini.

4. Ka sa bawanka yă yi murna, ya Ubangiji,Saboda addu'o'ina sun hau zuwa gare ka.

5. Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara,Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu'a gare ka.

6. Ka ji addu'ata, ya Ubangiji,Ka ji kukana na neman taimako!

7. Nakan kira gare ka a lokacin wahala,Saboda kakan amsa addu'ata.

8. Ba wani allah kamarka, ya Ubangiji,Ba ko ɗaya, ba wanda zai iya aikata abin da kake aikatawa.

9. Dukan sauran al'umma da ka halittaZa su zo su rusuna har ƙasa a gabanka.Za su yabi girmanka,

10. Gama kai kaɗai ne Maɗaukaki, ya Allah,Kai kaɗai ne ka aikata abubuwa na banmamaki.

11. Ya Ubangiji, ka koya mini abin da kake so in yi,Ni kuwa zan yi maka biyayya da aminci.Ka koya mini in bauta maka da zuciya ɗaya.

12. Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji Allahna,Zan riƙa shelar girmanka har abada.

13. Wane irin girma madawwamiyar ƙaunarka take da shi a gare ni!Gama ka cece ni daga zurfin kabari.

14. Masu girmankai sun tasar mini, ya Allah,Ƙungiyar mugaye tana ƙoƙari ta kashe ni,Mutanen da ba su kula da kai ba.

15. Ya Ubangiji, kai Allah ne mai jinƙai, mai ƙauna,Mai jinkirin fushi, kullum kai mai alheri ne, mai aminci.

16. Ka juyo gare ni, ka yi mini jinƙai,Ka ƙarfafa ni, ka cece ni,Gama ina bauta maka, kamar yadda mahaifiyata ta yi.

17. Ka nuna mini alherinka, ya Ubangiji,Sa'an nan su waɗanda suke ƙina za su sha kunya,Sa'ad da suka ga ka ta'azantar da ni,Ka kuma taimake ni.