Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 46 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Annabci a kan Masar

1. Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan sauran al'umma.

2. Ya yi magana game da sojojin Fir'auna, Sarkin Masar, waɗanda suke a bakin Kogin Yufiretis a Karkemish, waɗanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya ci su da yaƙi a shekara ta huɗu ta sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza.

3. Masarawa suka yi ihu, suka ce,“Ku shirya kutufani da garkuwa,Ku matso zuwa wurin yaƙi!

4. Ku ɗaura wa dawakanku sirdi, kuhau!Ku tsaya a wurarenku da kwalkwalia ka!Ku wasa māsunku!Ku sa kayan yaƙi!”

5. Ubangiji ya yi tambaya ya ce,“Me nake gani?Sun tsorata, suna ja da baya,An ci sojojinsu, suna gudu,Ba su waiwayen baya, akwai tsoro akowane sashi.”

6. Masu saurin gudu ba za su tsere ba,Haka nan kuma jarumi,A arewa a gefen Kogin Yufiretis,Sun yi tuntuɓe, sun fādi.

7. Wane ne wannan mai tashi kamarKogin Nilu,Kamar kogunan da ruwansu yakeambaliya?

8. Masar tana tashi kamar Nilu,Kamar kogunan da ruwansu yakeambaliya.Masar ta ce, “Zan tashi, in rufeduniya,Zan hallaka birane da mazaunacikinsu.”

9. Ku haura, ku dawakai,Ku yi sukuwar hauka, ku karusai!Bari sojoji su fito,Mutanen Habasha da Fut masuriƙon garkuwoyi,Da mutanen Lud, waɗanda suka iyariƙon baka.

10. Wannan rana ta Ubangiji, Allah MaiRunduna ce,Ranar ɗaukar fansa ce don ya ramawa maƙiyansa.Takobi zai ci, ya ƙoshi,Ya kuma sha jininsu, ya ƙoshi,Gama Ubangiji Allah Mai Rundunazai hallaka maƙiyansa,A arewa, a bakin Kogin Yufiretis.

11. Ku mutanen Masar, ku haura zuwaGileyadDon ku samo ganye!A banza kuke morar magunguna,Ba za ku warke ba.

12. Kunyarku ta kai cikin sauranal'umma,Kukanku kuma ya cika duniya.Soja na faɗuwa bisa kan soja.Dukansu biyu sun faɗi tare.

13. Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan zuwan Nebukadnezzar, Sarkin Babila, don ya yi yaƙi da ƙasar Masar.

14. “Ku yi shelarsa cikin garuruwanMasar,Cikin Migdol, da Memfis, daTafanes,Ku ce, ‘Ku tsaya, ku yi shiri,Gama takobi yana cin waɗanda sukekewaye da ku!’

15. Me ya sa gunkinka, Afis, ya fāɗi,Wato bijimi, gunkinka bai tsaya ba?Domin Ubangiji ya tunkuɗe shiƙasa!

16. Sun yi ta fāɗuwa,Suna faɗuwa a kan juna,Sai suka ce, ‘Mu tashi mu komawurin mutanenmu,Zuwa ƙasar haihuwarmu, mu gududaga takobin azzalumi!’

17. “Ku ba Fir'auna Sarkin Masarsabon suna,‘Mai yawan surutu, wanda bai rifcizarafi ba!’

18. Ni wanda sunana Ubangiji MaiRunduna Sarki ne,Na rantse da raina, wani zai ɓullo,Kamar Tabor a cikin tsaunuka,Ko kuwa kamar Karmel a bakinteku.

19. Ya ku mazaunan Masar,Ku shirya kayanku don zuwa bauta,Gama Memfis za ta lalace, ta zamakufai,Ba mai zama a ciki.

20. “Masar kyakkyawar karsana ce,Amma bobuwa daga arewa ta aukarmata!

21. Sojojin ijararta kamar 'yan maruƙane, masu yawan kitse,Sun ba da baya, sun gudu, ba sutsaya ba,Domin ranar masifarsu ta zo,Lokacin halakarsu ya yi.

22. Masar tana gudu, tana huci kamarmaciji,Gama abokan gābanta suna zuwa daƙarfi,Za su faɗo mata da gatura kamarmasu saran itatuwa.

23. Ni Ubangiji na ce, za su sarikurminta,Ko da yake ba su ƙirguwa,Gama suna da yawa kamar fara,Ba su lasaftuwa.

24. Za a kunyatar da mutanen Masar,An bashe su a hannun mutanenarewa.”

25. Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, “Ga shi, zan hukunta Amon na No, da Fir'auna, da Masar, tare da allolinta, da sarakunanta, wato Fir'auna, tare da waɗanda suke dogara gare shi.

26. Zan bashe su a hannun waɗanda suke neman ransu, wato a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da shugabanninsa. Daga baya kuma mutane za su zauna a Masar kamar dā. Ni Ubangiji na faɗa.

27. “Ya bawana Yakubu, kada ka jitsoro,Kada ka firgita, ya Isra'ila.Gama zan cece ka daga ƙasa mainisa,Zan ceci zuriyarka daga ƙasarbautarsu.Yakubu zai komo, ya yi zamansa darai kwance,Ba wanda zai razanar da shi.

28. Ni Ubangiji na ce,Kada ka ji tsoro, ya bawanaYakubu,Gama ina tare da kai.Zan hallaka dukan sauran al'ummasarai inda na kora ka.Amma ba zan hallaka ka sarai ba.Zan hukunta ka yadda ya kamata,Ba zan bar ka ba hukunci ba.”