Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 50 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Jawabin Ubangiji a kan Babila

1. Jawabin da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kanBabila da ƙasar Kaldiyawa ke nan,

2. “Ku ba da labari ga sauranal'umma, ku yi shela,Ku ta da tuta, ku yi shela,Kada ku ɓuya, amma ku ce,‘An ci Babila da yaƙi,An kunyatar da Bel,An kunyatar da siffofinta,Merodak ya rushe,Gumakanta kuma sun ragargaje!’

3. “Wata al'umma za ta taso daga arewa gāba da ita, za ta mai da ƙasar abar ƙyama, ba wanda zai zauna ciki. Mutum da dabba duk sun watse, kowa ya bar ta.”

4. Ubangiji ya ce, “Sa'ad da lokacin nan ya yi, mutanen Isra'ila da na Yahuza za su zo tare, suna kuka, suna nemana, ni Ubangiji Allahnsu.

5. Za su tambayi hanyar Sihiyona, sa'an nan su bi ta, suna cewa, ‘Bari mu haɗa kanmu don mu yi madawwamin alkawari da Ubangiji, alkawari wanda ba za a manta da shi ba.’

6. “Mutanena sun zama kamar ɓatattuntumaki,Waɗanda makiyayansu suka bauɗarda su,Suka ɓata a cikin tsaunuka,Suna kai da kawowa daga wannandutse zuwa wancan.Sun manta da shingensu.

7. Duk waɗanda suka same su, suncinye su.Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifiba,’Gama sun yi wa Ubangiji laifi,wanda yake tushen gaskiya,Ubangiji wanda kakanninsu sukadogara gare shi.

8. “Ku gudu daga cikin Babila,Ku fita kuma daga cikin ƙasarKaldiyawa,Ku zama kamar bunsurai waɗandasuke ja gaban garke.

9. Ga shi, zan kuta manyan ƙasashedaga arewaSu faɗa wa Babila da yaƙi.Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, sucinye ta.Kibansu kamar na gwanayenmayaƙa neWaɗanda ba su komowa banza.

10. Za a washe Kaldiyawa,Waɗanda suka washe su kuwa za suƙoshi,Ni Ubangiji na faɗa.

11. “Saboda kuna murna, kuna farinciki,Ku da kuka washe gādona,Saboda kuma kuna tsalle kamarkarsana a cikin ciyawa,Kuna haniniya kamar ingarmu,

12. Domin haka za a kunyatar da Babilasosai, inda kuka fito.Za ta zama ta baya duka a cikinsauran al'umma,Za ta zama hamada, busasshiyarƙasa.

13. Saboda fushin Ubangiji, ba wandazai zauna a cikinta,Za ta zama kufai,Duk wanda ya bi ta wajen Babila, zaiji tsoro,Zai kuma yi tsaki sabodalalacewarta.

14. “Dukanku 'yan baka, ku ja dāga, kukewaye Babila,Ku harbe ta, kada ku rage kibanku,Gama ta yi wa Ubangiji zunubi.

15. Ku kewaye ta da kuwwar yaƙi!Ta ba da gari,Ginshiƙanta sun fāɗi.An rushe garunta,Gama wannan sakayya ce taUbangiji.Ku sāka mata, ku yi mata kamaryadda ta yi.

16. Ku datse wa Babila mai shuka,Da mai yanka da lauje a lokacingirbi.Saboda takobin azzalumi,Kowa zai koma wurin mutanensa,Kowa kuma zai gudu zuwaƙasarsa.”

17. “Isra'ilawa kamar tumaki ne waɗanda zakuna suka bi su suna kora. Da farko dai Sarkin Assuriya ne ya cinye su. Yanzu kuwa Sarkin Babila, wato Nebukadnezzar, shi ne yake gaigayi ƙasusuwansu.

18. Saboda haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila na ce, zan yi wa Sarkin Babila da ƙasarsa hukunci, kamar yadda na hukunta Sarkin Assuriya.

19. Zan komar da Isra'ila a makiyayarsa, zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Zai sami biyan bukatarsa a tsaunukan Ifraimu da na Gileyad.

20. Ni Ubangiji na ce sa'ad da lokacin nan ya yi za a nemi laifi da zunubi a cikin Isra'ila da Yahuza, amma ba za a samu ba, gama zan gafarta wa sauran da suka ragu.

21. “Ku haura ku fāɗa wa ƙasarMeratayim da mazaunan Fekod.Ku kashe, ku hallaka su sarai,Ku aikata dukan abin da na umarceku,Ni Ubangiji na faɗa.

22. Hargowar yaƙi tana cikin ƙasar,Da kuma babbar hallakarwa!

23. Ga yadda aka karya gudumar dukanduniya!Ga yadda Babila ta zama abarƙyama ga sauran al'umma!

24. Na kafa miki tarko, ya kuwa kamaki, ya Babila,Ke kuwa ba ki sani ba.An same ki, an kama,Domin kin yi gāba da ni.”

25. Ubangiji ya buɗe taskarmakamansa,Ya fito da makaman hasalarsa,Gama Ubangiji Allah Mai Rundunayana da aikin da zai yi a ƙasarKaldiyawa.

26. Ku zo, ku fāɗa mata daga kowanesashi.Ku buɗe rumbunanta,Ku tsittsiba ta kamar tsibin hatsi,Ku hallakar da ita ɗungum,Kada wani abu nata ya ragu.

27. Ku kashe dukan bijimanta, a kai sumayanka!Kaitonsu, gama kwanansu ya ƙare,Lokacin hukuncinsu ya yi.

28. Ku ji, sun gudu sun tsere daga ƙasarBabila,Don su faɗa cikin Sihiyona,Sakayyar Ubangiji Allahnmu dominHaikalinsa.

29. “Ku kirawo 'yan baka, dukanwaɗanda sukan ja baka, su faɗawa Babila.Ku kafa sansani kewaye da ita, kadaku bar kowa ya tsira.Ku sāka mata bisa ga dukanayyukanta, gama ta raina UbangijiMai Tsarki na Isra'ila.

30. Domin haka samarinta za su fāɗi atituna.Za a hallaka sojojinta duka a wannanrana,Ni Ubangiji na faɗa.

31. “Ga shi, ina gāba da ke, ke Babila,mai girmankai.Gama ranar da zan hukunta ki, ta zo,Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.

32. Mai girmankai za ta yi tuntuɓe tafāɗi,Ba kuwa wanda zai tashe ta,Zan ƙone garuruwanta da wuta,Zan kuma hallaka dukan abin da yakekewaye da ita.

33. “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce,An danne mutanen Isra'ila da naYahuza,Duk waɗanda suka kama su bayi sunriƙe su da ƙarfi.Sun ƙi su sake su.

34. Mai fansarsu mai ƙarfi ne,Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.Hakika zai tsaya musu don ya kawowa duniya salama,Amma zai kawo wa mazaunan Babilafitina.

35. Ni Ubangiji na ce,Akwai takobi a kan Kaldiyawa,Da a kan mazaunan Babila,Da a kan ma'aikatanta da masuhikimarta,

36. Akwai takobi a kan masu sihiriDon su zama wawaye.Akwai takobi a kan jarumawantaDon a hallaka su.

37. Akwai takobi a kan mahayandawakanta, da a kan karusanta,Da a kan sojojin da ta yi ijara da suDon su zama kamar mata,Akwai takobi a kan dukan dukiyartadomin a washe ta.

38. Fari zai sa ruwanta ya ƙafe,Gama ƙasa tana cike da gumakawaɗanda suka ɗauke hankalinmutane.

39. “Domin haka namomin jeji da diloliza su zauna a Babila,Haka kuma jiminai.Ba za a ƙara samun mazauna acikinta ba har dukan zamanai.

40. Abin da ya faru da Saduma daGwamrata,Da biranen da suke kewaye da su,Shi ne zai faru da Babila.Ba mutumin da zai zauna cikinta.

41. “Ga mutane suna zuwa daga arewa,Babbar al'umma da sarakunaSuna tahowa daga wurare masu nisana duniya.

42. Suna riƙe da baka da māshi,Mugaye ne marasa tausayi.Amonsu yana kama da rurin teku,Suna shirya don yin yaƙi da ke, yaBabila.

43. Sarkin Babila ya ji labarinsu,Hannuwansa suka yi suwu.Wahala da azaba sun kama shikamar mace mai naƙuda.

44. “Ni Ubangiji ina zuwa kamar zakin da yake fitowa daga kurmin Urdun zuwa makiyaya. Nan da nan zan sa su gudu daga gare ta. Sa'an nan zan naɗa mata wanda na zaɓa. Wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Wane shugaba zai yi gāba da ni?

45. Saboda haka ku ji shirin da Ubangiji ya yi gāba da Babila, da nufin ya yi gaba da ƙasar Kaldiyawa. Hakika za a tafi da ƙananansu, garke zai zama kango.

46. Duniya za ta girgiza sa'ad da ta ji an ci Babila da yaƙi. Za a ji kukanta cikin sauran al'umma.”