Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Tabbatarwar Komowa daga Zaman Talala

1. Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce,

2. “Ni Ubangiji Allah na Isra'ila na ce, ‘Ka rubuta dukan maganar da na faɗa maka a littafi.

3. Gama kwanaki suna zuwa sa'ad da zan komo da mutanena, wato Isra'ila da Yahuza. Zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu, za su kuwa mallake ta,’ ni Ubangiji na faɗa.”

4. Waɗannan ne maganar da Ubangiji ya faɗa a kan Isra'ila da Yahuza.

5. “Ni Ubangiji na ce,Mun ji kukan gigitacce,Kukan firgita ba kuma salama.

6. Yanzu ku tambaya, ku ji,Namiji ya taɓa haihuwa?To, me ya sa nake ganin kowanenamiji yana riƙe da kwankwaso,Kamar mace mai naƙuda,Fuskar kowa kuma ta yi yaushi?

7. Kaito, gama wannan babbar rana ce,Ba kuma kamarta,Lokaci ne na wahala ga Yakubu,Duk da haka za a cece shi dagacikinta.”

8. Ubangiji Mai Runduna ya ce, “A wannan rana zan karya karkiya da take a wuyansu, in cire musu ƙangi, ba kuma za su ƙara zama bayin baƙi ba.

9. Amma za su bauta mini, ni Ubangiji Allahnsu, da Dawuda sarkinsu, wanda zan tayar musu da shi.”

10. Ubangiji ya ce,“Kada ka ji tsoro, ya baranaYakubu,Kada kuma ka yi fargaba, yaIsra'ila,Gama zan cece ka daga ƙasa mainisa,Zan kuma ceci zuriyarka daga ƙasarbautarsu.Yakubu zai komo, ya yi zamansa raia kwance,Ba kuwa za a tsoratar da shi ba.

11. Gama ina tare da kai don in cece ka,Zan hallaka dukan al'ummai sarai,Inda na warwatsa ku.Amma ku ba zan hallaka ku ba,Zan hore ku da adalci,Ba yadda za a yi in ƙyale ku bahukunci,Ni Ubangiji na faɗa.”

12. Ubangiji ya ce,“Rauninku ba ya warkuwa,Mikinku kuwa mai tsanani neƙwarai.

13. Ba wanda zai kula da maganarku,Ba magani domin mikinku,Ba za ku warke ba.

14. Dukan masu ƙaunarku sun mantada ku,Ba su ƙara kulawa da ku,Domin na yi muku bugu irin namaƙiyi.Na yi muku horo irin na maƙiyimarar tausayi,Domin laifofinku masu girma ne,Domin zunubanku da yawa suke.

15. Don me kuke kuka a kanrauninku?Ciwonku ba zai warke ba.Saboda laifofinku masu girma ne,Domin zunubanku da yawa suke,Shi ya sa na yi muku waɗannanabubuwa.

16. Domin haka dukan waɗanda sukacinye ku, za a cinye su,Dukan maƙiyanku, kowane ɗayansuzai tafi bauta,Waɗanda suka washe ku, za a washesu.Dukan waɗanda suka kwashe kuganima, su ma za a kwashe suganima.

17. Zan mayar muku da lafiyarku,Zan kuma warkar da raunukanku,Ko da yake maƙiyanku sunakiranku yasassu,Suna cewa, ‘Ai, Sihiyona ce, bawanda ya kula da ita.’Ni Ubangiji na faɗa.”

18. Ubangiji ya ce,“Ga shi, zan komar wa alfarwarYakubu arzikinta,Zan kuma nuna wa wuraren zamansajinƙai,Za a sāke gina birnin a kufansa,Fādar kuma za ta kasance a indatake a dā.

19. Daga cikinsu za a ji waƙoƙin godiya.Da muryoyin masu murna.Zai riɓaɓɓanya su, ba za su zamakaɗan ba,Zan kuwa ɗaukaka su, ba za aƙasƙantar da su ba.

20. 'Ya'yansu za su zama kamar dā,Jama'arsu kuma za su kahu agabana,Zan hukunta dukan waɗanda sukazalunce su.

21. Sarkinsu zai zama ɗaya dagacikinsu,Mai mulkinsu kuma zai fito dagacikinsu.Zan kawo shi kusa, zai kuwa kusaceni,Gama wane ne zai yi ƙarfin hali yakusace ni? Ni Ubangiji na faɗa.

22. Za ku zama mutanena,Ni kuwa zan zama Allahnku.”

23. Ga hadirin hasalar Ubangiji ya taso,wato iskar guguwa,Zai huce a kan mugaye.

24. Zafin fushin Ubangiji ba zai huce ba,Sai ya aikata, ya kammala abubuwanda ya yi niyya a tunaninsa.A nan gaba mutanensa za su fahimciwannan.