Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42
  43. 43
  44. 44
  45. 45
  46. 46
  47. 47
  48. 48
  49. 49
  50. 50
  51. 51
  52. 52

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce,“Ya mutanen Isra'ila, idan za kujuyo ku komo wurina,Idan kuka kawar da abubuwanbanƙyama daga gabana,Kuka kuma bar yin shakka,

2. Idan kun yi rantsuwa kuka ce,‘Har da ran Ubangiji kuwa,‘Da gaskiya, da aminci, da adalci,Sa'an nan sauran al'umma za su soin sa musu albarka,Za su kuma yabe ni.”

3. Ubangiji ya ce wa mutanen Yahuza da na Urushalima,“Ku kafce saurukanku,Kada ku yi shuka cikin ƙayayuwa.

4. Ya ku mutanen Yahuza da naUrushalima,Ku yi wa kanku kaciya dominUbangiji,Ku kawar da loɓar zukatankuDon kada fushina ya fito kamarwuta,Ya cinye, ba mai iya kashewa,Saboda mugayen ayyukan da kukaaikata.”

Yahuza tana cikin Barazanar Yaƙi

5. “Ku yi shela a cikin Yahuza,Ku ta da murya a Urushalima, kuce,‘Ku busa ƙaho a dukan ƙasar!’Ku ta da murya da ƙarfi, ku ce,‘Ku tattaru, mu shiga birane masugaru.’

6. Ku ta da tuta wajen Sihiyona!Ku sheƙa a guje neman mafaka,kada ku tsaya!Gama zan kawo masifa da babbarhalaka daga arewa.

7. Zaki ya hauro daga cikinruƙuƙinsa,Mai hallaka al'ummai ya kamahanya,Ya fito daga wurin zamansa don yamai da ƙasarku kufai,Ya lalatar da biranenku, su zamakango, ba kowa.

8. Domin haka sai ku sa tufafinmakoki,Ku yi makoki ku yi kuka,Gama fushin Ubangiji bai rabu damu ba.”

9. Ubangiji ya ce, “A ranan nan, sarki da sarakuna, za su rasa ƙarfin hali, firistoci za su firgita, annabawa kuwa za su yi mamaki.”

10. Sai na ce, “Kaito, kaito, ya Ubangiji Allah, ka ruɗi jama'an nan da Urushalima, da ka ce musu, ‘Za ku zauna lafiya,’ amma ga shi, takobi zai sassare su.”

11. Lokaci yana zuwa da za a faɗa wa mutanen Urushalima cewa, “Iska mai zafi za ta huro daga tuddan hamada zuwa wajen jama'ata, ba domin a sheƙe ta ko a rairaye ta ba!

12. Wannan iska da za ta zo daga wurin Ubangiji, tana da mafificin ƙarfi. Yanzu fa zan yanke hukunci a kansu.”

Abokan Gāba sun Kewaye Yahuza da Yaƙi

13. Duba, ga abokin gāba yana zuwakamar gizagizai,Karusan yaƙinsa suna kama daguguwa,Dawakansa sun fi gaggafa sauri.Kaitonmu, mun shiga uku!

14. Ya Urushalima, ki wanke muguntadaga zuciyarki,Domin a cece ki,Har yaushe mugayen tunaninki za suyi ta zama a cikinki?

15. Gama wata murya daga Dan tafaɗa,Ta kuma yi shelar masifar da za tafito daga duwatsun Ifraimu.

16. “A faɗakar da al'ummai, yana zuwa,A faɗa wa Urushalima cewa,‘Masu kawo mata yaƙi suna zuwadaga ƙasa mai nisa,Suna yi wa biranen Yahuza ihu.

17. Za su kewaye Yahuza kamar masutsaron saura,Saboda ta tayar wa Ubangiji.’ NiUbangiji na faɗa.

18. “Al'amuranki da ayyukanki sukajawo miki wannan halaka,Tana da ɗaci kuwa,Ta soki har can cikin zuciyarki.”

Irmiya ya yi Baƙin Ciki don Mutanensa

19. Azaba! Ba zan iya daurewa da azababa!Zuciyata! Gabana yana faɗuwa daƙarfi,Ba zan iya yin shiru ba,Gama na ji amon ƙaho da hargowaryaƙi.

20. Bala'i a kan bala'i,Ƙasa duka ta zama kufai,An lalatar da alfarwaina, ba zato batsammani,Labulena kuwa farat ɗaya.

21. Har yaushe zan yi ta ganin tuta,In yi ta jin amon ƙaho?

22. Ubangiji ya ce,“Mutanena wawaye ne,Ba su san ni ba,Yara ne dakikai,Ba su da ganewa.Suna gwanance da aikin mugunta,Amma ba su san yadda za su yinagarta ba.”

23. Da na duba duniya sai na ga kufai cekawai ba kome,Na kuma dubi sammai sai na ga bahaske.

24. Da na duba duwatsu, sai na ga sunamakyarkyata,Dukan tuddai kuma suna rawar jiki,su yi gaba su yi baya.

25. Na duba sai na ga ba ko mutumɗaya,Dukan tsuntsaye kuma sun tsere.

26. Na duba, sai na ga ƙasa mai dausayita zama hamada,An mai da dukan biranentakangwayeA gaban Ubangiji saboda zafinfushinsa.

27. Gama Ubangiji ya ce, “Ƙasar duka za ta zama kufai, amma duk da haka, ba wannan ne zai zama ƙarshenta na har abada ba.

28. Duniya za ta yi makoki sabodawannan,Sammai za su duhunta,Gama ni na faɗa, haka kuwa na nufain yi,Ba zan ji tausayi ba,Ba zan kuwa fāsa ba.”

29. Da jin motsin mahayan dawakai dana maharbaKowane gari zai fashe.Waɗansu za su shiga kurama,Waɗansu kuma su hau kan duwatsu.Dukan birane za su fashe tas,Ba wanda zai zauna a cikinsu.

30. Ya ke da kike kufai marar kowa,Me kike nufi da kika ci ado da mulufi,Kike caɓa ado da kayan zinariya,Kika sa wa idanunki tozali ram?Kin yi kwalliyarki a banza,Abokan sha'anin karuwancinki sunraina ki,Ranki suke nema.

31. Na ji kuka kamar na mace wadda takenaƙuda,Na ji nishi kamar na mace a lokacinhaihuwarta ta fari,Na ji kukan 'yar Sihiyona tanakyakyari,Tana miƙa hannuwanta tana cewa,“Wayyo ni kaina, gama ina suma agaban masu kisankai!”