Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Ayuba Ya Zargi Abokansa

1. Ayuba ya amsa.

2. “In da za a auna wahalata da ɓacin raina da ma'auni,

3. Da sun fi yashin teku nauyi.Kada ka yi mamaki da maganganun da nake yi.

4. Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau,Dafinsu kuwa ya ratsa jikina.Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana.

5. “Idan jaki ya sami ciyawar ci, muradinsa ya biya,In ka ji saniya ta yi shiru, tana cin ingirici ne.

6. Amma wane ne zai iya cin abinci ba gishiri?Akwai daɗin ɗanɗano ga farin ruwan ƙwai?

7. Ba na jin marmarin cin abinci irin haka,Kowane irin abu da na ci yakan sa mini cuta.

8. “Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo?Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so?

9. Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni,Ko ya sake ikonsa ya datse ni!

10. Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna,Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba.Ban taɓa yin gāba da umarnan Allah ba.

11. Wane ƙarfi ne nake da shi na rayuwa?Wane sa zuciya kuma nake da ita,tun da na tabbata mutuwa zan yi?

12. Da dutse aka yi ni?Ko da tagulla aka yi jikina?

13. Ba ni da sauran ƙarfi da zan ceci kaina,Ba inda zan juya in nemi taimako.

14. “A cikin irin wannan wahalaIna bukatar amintattun abokai,Ko da na rabu da Allah, ko ina tare da shi.

15. Amma ku abokaina,kun ruɗe ni,Kamar rafi wanda yakan ƙafe da rani.

16-17. Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara,Amma lokacin zafi sai su ɓace,Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome.

18. Ayari sukan ɓata garin neman ruwa,Su yi ta gilo, har su marmace a hamada.

19. Ayari daga Sheba da Tema suka yi ta nema,

20. Amma sa zuciyarsu ta ƙare a gefen busassun rafuffuka,

21. Kamar rafuffukan nan kuke a gare ni,Kun ga abin da ya same ni, kun gigita.

22. Na roƙe ku ku ba ni kyauta ne?Ko kuwa na roƙe ku ku ba wani rashawa domina?

23. Ko kuma na roƙe ku ku cece ni daga maƙiyi ko azzalumi ne?

24. “To, sai ku koya mini, ku bayyana mini laifofina,Zan yi shiru in kasa kunne gare ku.

25. Kila muhawara mai ma'ana ta rinjaye ni,Amma yanzu duk maganar shirme kuke yi.

26. Kuna so ku amsa maganganuna?Don me?Mutumin da yake cikin halin ƙaƙa naka yi,Ba wata maganar da zai yi in ba shirme ba.

27. Kukan jefa wa bayi da marayu kuri'a,Kukan arzuta kanku daga abokanku na kurkusa.

28. Ku dubi fuskata,Lalle ba zan faɗi ƙarya ba.

29. Kai, kun zaƙe, ku daina aikata rashin adalci,Kada ku sa mini laifi, nake da gaskiya.

30. Amma duk da haka kuna tsammani ƙarya nake yi.Kuna tsammani ba zan iya rarrabe tsakanin gaskiya da ƙarya ba.”