Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Elifaz ya Zargi Ayuba a kan Aikata Mugunta

1. Elifaz ya yi magana.

2. “Akwai wani mutum, ko mafi hikima,Wanda zai amfani Allah?

3. Gaskiyar da kake yi za ta amfani Allah?Ko kuwa abin kirki da kake yi zai taimake shi?

4. Ai, ba don tsoron Allah da kake yi ba ne,Ya sa wannan tsautawa da jarrabawa suka same ka.

5. Ko kusa ba haka ba ne,Amma saboda zunubi mai yawa da ka yi ne.Saboda kuma dukan muguntar da ka aikata.

6. Don ka sa ɗan'uwanka ya biya ka bashin da kake binsa,Ka ƙwace tufafinsa, ka bar shi huntu.

7. Ka hana wa waɗanda suke ji ƙishi ruwan sha,Ka hana waɗanda suke jin yunwa abinci.

8. Ka mori ikonka da matsayinka,Don ka mallaki dukan ƙasar.

9. Ba ƙin taimako kaɗai ka yi ba,Amma har marayu ma ka yi musu ƙwace, ka wulakanta su.

10. Don haka ne yanzu akwai ramummuka ko'ina kewaye da kai,Tsoro ya kama ka nan da nan.

11. An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani,Rigyawa ta sha kanka.

12. “Ashe, ba a can saman sammai Allah yake zaune ba?Sai ya sunkuya ya dubi taurari, ko da yake suna can sama ne.

13. Duk da haka ka ce, ‘Allah bai san kome ba.Gizagizai sun lulluɓe shi, ƙaƙa zai iya yi mana shari'a?’

14. Kana tsammani gizagizai masu duhu sun hana shi gani,A lokacin da yake tafiya a kan iyakar da take tsakanin duniya da sararin sama.

15. “Ka ɗauka a ranka ka bi gurbin da mugaye suke bi kullum?

16. Kafin ma su kai ga kwanakinsu,Sai rigyawa ta shafe su.

17. Su ne mutanen da suka ƙi Allah,Suka kuwa gaskata ba shi da ikon yi musu kome,

18. Ko da yake Allah ne ya arzuta su.Ba na iya gane tunanin mugaye.

19. Mutanen kirki suna murna,Marasa laifi kuma suna dariyaSa'ad da suka ga ana hukunta mugaye.

20. Duk abin da mugu ya mallaka ya hallaka,Wuta kuwa ta lashe kowane abu da ya ragu.

21. “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah,Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka,In ka yi haka, to, za ka sami albarka.

22. Ka karɓi koyarwar da yake yi,Ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.

23. Hakika sai ka yi tawali'u, ka koma wurin Allah,Ka kawar da dukan muguntar da ake yi a gidanka.

24. Ka jefar da zinariyarka, zinariyarka mafi kyau,Ka jefar da ita kamar dutse ko ƙura.

25. Bari Allah Mai Iko Dukka ya zama zinariyarka,Ya zama azurfa, wadda aka tula dominka.

26. Sa'an nan za ka dogara ga Allah kullayaumin,Ka kuma tarar shi ne asalin farin cikinka.

27. Sa'ad da ka yi addu'a zai amsa maka,Za ka kuwa kiyaye alkawaran da ka yi.

28. Za ka yi nasara a kowane abu da za ka yi,Haske kuma zai haskaka hanyarka.

29. Allah yakan ƙasƙantar da mai girmankai,Yakan ceci mai tawali'u.

30. Zai ceci wanda yake da laifi,Idan abin da kake yi daidai ne.”