Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 37 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Saboda wannan zuciyata takan kaɗu,Kamar ta yi tsalle daga inda take.

2. Ku kasa kunne ga tsawar muryarsa,Ku saurara ga maganarsa mai ƙarfi.

3. Yakan sako ta a ƙarƙashin samaniya duka,Walƙiyarsa takan zagaya dukan kusurwoyin duniya.

4. Bayan walƙiyar akan ji rugugin muryarsa,Ya yi tsawa da muryarsa ta ɗaukaka,Ko da yake an ji muryarsa bai dakatar da tsawar ba.

5. Muryar tsawar Allah mai banmamaki ce,Yana aikata manyan abubuwa da suka fi ƙarfin ganewarmu.

6. Yakan umarci dusar ƙanƙara ta fāɗo bisa duniya,Yayyafi da ruwan sama kuwa su yi ƙarfi.

7. Yakan tsai da kowane mutum daga aikinsa,Domin dukan mutane su san aikinsa.

8. Namomin jeji sukan shiga wurin kwanciyarsu,Su yi zamansu a ciki.

9. Guguwa takan taso daga inda take,Sanyi kuma daga cikin iska mai hurawa.

10. Numfashin Allah yakan sa ƙanƙara,Yakan sa manyan ruwaye su daskare farat ɗaya.

11. Yakan cika girgije mai duhu da ruwa,Gizagizai sukan baza walƙiyarsa.

12. Sukan yi ta kewayawa ta yadda ya bishe su,Don su cika dukan abin da ya umarce su a duniya da ake zaune a ciki.

13. Allah yakan aiko da ruwan sama ya shayar da duniya,Saboda tsautawa, ko saboda ƙasa, ko saboda ƙauna.

14. “Ka ji wannan, ya Ayuba,Tsaya ka tuna da ayyukan Allah masu banmamaki.

15. Koka san yadda Allah yakan ba su umarni,Ya sa walƙiyar girgijensa ta haskaka?

16. Ko kuma ka san yadda gizagizai suke tsaye daram a sararin sama?Ayyukan banmamaki na Allah, cikakken masani!

17. Ko ka san abin da yake sa ka jin gumiSa'ad da iskar kudu take hurowa?

18. Ka iya yin yadda ya yi,Kamar yadda ya shimfiɗa sararin sama daram,Kamar narkakken madubi?

19. Ka koya mana abin da za mu faɗa masa,Ba za mu iya gabatar da ƙararrakinmu ba, gama mu dolaye ne.

20. A iya faɗa masa, cewa zan yi magana?Mutum ya taɓa so a haɗiye shi da rai?

21. “A yanzu dai mutane ba su iya duban haske,Sa'ad da yake haskakawa a sararin sama,Bayan da iska ta hura ta share gizagizai sarai.

22. Daga arewa wani haske kamar na zinariya ya fito mai banmamaki,Allah yana saye da ɗaukaka mai bantsoro.

23. Mai Iko Dukka, ya fi ƙarfin ganewarmu,Shi mai girma ne, da iko, da gaskiya,Da yalwataccen adalci,Ba ya garari.

24. Saboda haka mutane suke tsoronsa,Bai kula da waɗanda suke ɗaukar kansu su masu hikima ba ne.”