Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Ayuba Ya Kāre Mutuncinsa

1-2. “Duk abin da ka hurta, na taɓa jinsa,Na gane da shi sarai.Iyakar abin da kuka sani, ni ma na sani.Ba ku fi ni da kome ba.

3. Amma da Allah nake jayayya, ba da ku ba,Ina so in yi muhawara da shi a kan ƙarar da nake da ita.

4. Kun ɓoye jahilcinku da ƙarairayi.Kun zama kamar likitoci waɗanda ba su iya warkar da kowa ba.

5. Kada ku faɗi kome,Wani sai ya ce kuna da hikima!

6. “Ku saurara mini, zan faɗi ƙarata.

7. Me ya sa kuke yin ƙarya?Kuna tsammani ƙarairayinku za su taimaki Allah?

8. Son zuciya kuke yi, ko ba haka ba?Kuna goyon bayan Allah?Za ku goyi bayan Allah sa'ad da aka gurfanar da ni gaban shari'a?

9. Da Allah ya bincike ku sosai,Zai iske wani abin kirki ne a cikinku?Kuna tsammani za ku ruɗi Allah, kamar yadda kuke ruɗin mutane?

10. Ko da yake kun ɓoye son zuciyarku,Duk da haka zai tsauta muku,

11. Ikonsa kuwa zai razana ku.

12. Karin maganarku da muhawararku ba su da ƙarfi ƙwarai.

13. “Ku yi shiru ku ba ni zarafi in yi magana.Duk abin da zai faru, ya faru.

14. A shirye nake in yi kasai da raina.

15. Na fid da zuciya ɗungum.To, in Allah ya kashe ni, sai me?Zan faɗa masa ƙarata.

16. Mai yiwuwa ne ƙarfin halina ya cece ni,Tun da yake ba wani mugun mutumin da zai iya zuwa gaban Allah.

17. Sai a saurari bayanin da zan yi.

18. A shirye nake in faɗi ƙarata,Domin na sani ina da gaskiya.

19. “Ya Allah, za ka yi ƙarata?Idan kuwa ka yi, to, a shirye nake in yi shiru in mutu.

20. Ina da abu biyu da zan yi maka roƙo,Ka yarda da su, sa'an nan ba zan yi ƙoƙari in ɓoye ba.

21. Wato ka daina hukuncin da kake yi mini,Kada ka sa razanarka ta ragargaza ni.

22. “Ka fara yin magana, ya Allah, ni kuwa zan amsa.Ko kuma ka bari in yi magana, sa'an nan ka amsa mini.

23. Kuskure da laifi guda nawa na yi?Waɗanne irin laifofi ake tuhumata da su?

24. Me ya sa kake guduna?Me ya sa ka maishe ni kamar maƙiyi?

25. Ƙoƙari kake ka firgita ni?Ni ba wani abu ba ne, ganye ne kawai,Ka fāɗa wa tattaka da yaƙi ne kawai.

26. Ka kawo mugayen ƙararraki a kaina,Har da laifofin da na yi na ƙuruciya.

27. Ka ɗaure ƙafata da sarƙoƙi,Kakan lura da kowace takawata,Har kana bin diddigin sawayena.

28. Saboda wannan na zama abin kallo,ni kuwa kamar ragargazajjen itace ne, ko diddigaggiyar riga.”