Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25
  26. 26
  27. 27
  28. 28
  29. 29
  30. 30
  31. 31
  32. 32
  33. 33
  34. 34
  35. 35
  36. 36
  37. 37
  38. 38
  39. 39
  40. 40
  41. 41
  42. 42

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ayu 24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Ayuba Ya Yi Kuka da Yake Allah Bai Kula da Mugunta Ba

1. “Me ya sa Allah bai tsai da ranar da zai yi shari'a ba?Me ya sa ba ya tsai da ranar adalci gaWaɗanda suka bauta masa?

2. Mugaye sukan ci iyaka,Don su ƙara yawan gonarsu.Sukan saci tumaki su zuba cikin garkunansu.

3. Sukan saci jakunan marayu,Su kama san gwauruwa,Su ce sai ta biya basusuwanta.

4. Sukan hana matalauta samun halaliyarsu,Sukan tilasta wa masu bukata su gudu su ɓuya.

5. Kamar jakunan jeji waɗanda sukan nemi abinci a busasshen jeji,Haka matalauta suke,Ba inda za su iya samo wa 'ya'yansu abinci.

6. Ya zama tilas a gare su su girbe gonakin da ba nasu ba,Su tattara 'ya'yan inabi daga gonakin mugaye.

7. Da dare sukan kwanta, ba su da abin rufa,Ba su da abin da zai hana su jin sanyi.

8. Sukan jiƙe sharkaf da ruwan sama wanda yake kwararowa daga kan duwatsu.Sun takure a gefen duwatsu neman mafaka.

9. “Mugaye sukan bautar da yara marayu,Sukan kama 'ya'ya matalauta a bakin bashin da suke bi.

10. Amma tilas matalauta su fita huntaye, ba sa da abin sutura.Tilas su girbi alkama suna kuwa jin yunwa.

11. Suna matse mai daga 'ya'yan zaitun.Suna kuma matse ruwan inabi daga 'ya'yan inabi,Amma su kansu suna fama da ƙishi.

12. Kana jin kukan waɗanda suka yi rauni daWaɗanda suke baƙin mutuwa a birni,Amma Allah bai kula da addu'o'insu ba.

13. “Akwai mugaye waɗanda suke ƙin haske,Ba su fahimce shi ba, suka ƙi bin hanyarsa.

14. Da asuba mai kisankai yakan fita ya kashe matalauci,Da dare kuma ya yi fashi.

15. Mazinaci yakan jira sai da magariba,Sa'an nan ya ɓoye fuskarsa don kada a gane shi.

16. Da dare ɓarayi sukan kutsa kai cikin gidaje,Amma da rana sukan ɓuya, su guje wa haske.

17. Gama tsananin duhu kamar safiya yake gare su,Sun saba da razanar duhu.

18. “Rigyawa takan ci mugun mutum,Ƙasar da ya mallaka kuwa tana ƙarƙashin la'anar Allah.Ba ya kuma iya zuwa aiki a gonar inabinsa.

19. Kamar dusar ƙanƙara take a lokacin zafi da a lokacin fari,Haka mai zunubi yakan shuɗe daga ƙasar masu rai.

20. Ba wanda zai tuna da shi,mahaifiyarsa ma ba za ta lura da shi ba.Tsutotsi sukan ci shi su hallaka shi sarai.Za a sare mugunta kamar itace.

21. Haka yake samun wanda ya wulakanta gwauraye.Bai kuma nuna alheri ga matan da ba su haihu ba.

22. Allah, da ikonsa, yakan hallaka masu ƙarfi,Allah yakan aikata, sai mugun mutum ya mutu.

23. Ya yiwu Allah ya bar shi ya yi zamansa lafiya,Amma a kowane lokaci zai sa ido a kansa.

24. Mugun mutum yakan ci nasara ɗan lokaci,Daga nan sai ya yi yaushi kamar tsiro,Ya yi yaushi kamar karan dawa da aka yanke.

25. Akwai wanda zai iya cewa, ba haka ba ne?Akwai wanda zai tabbatar da cewa kalmomina ba gaskiya ba ne?”