Surori

  1. 1
  2. 2
  3. 3
  4. 4
  5. 5
  6. 6
  7. 7
  8. 8
  9. 9
  10. 10
  11. 11
  12. 12
  13. 13
  14. 14
  15. 15
  16. 16
  17. 17
  18. 18
  19. 19
  20. 20
  21. 21
  22. 22
  23. 23
  24. 24
  25. 25

Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sar 17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

Faɗuwar Samariya da Bautar Isra'ila

1. A shekara ta goma sha biyu ta sarautar Ahaz Samariya Yahuza, Hosheya ɗan Ila ya ci sarautar Isra'ila a Samariya. Ya yi mulki shekara tara.

2. Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar sauran sarakunan Isra'ila da suka riga shi ba.

3. Sai Shalmanesar Sarkin Assuriya, ya kawo masa yaƙi, Hosheya kuwa ya zama talakansa, yana kai masa haraji.

4. Amma Sarkin Assuriya ya gane Hosheya ya tayar masa, gama ya aiki manzanni wurin So, wato Sarkin Masar, ya kuma ƙi ya kai wa Sarkin Assuriya haraji kamar yadda ya saba yi kowace shekara, Saboda haka sai Sarkin Assuriya ya kama shi ya sa shi a kurkuku.

5. Sa'an nan Sarkin Assuriya ya kai wa dukan ƙasar yaƙi, har ya kai Samariya. Ya kewaye Samariya da yaƙi shekara uku.

6. A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, Sarkin Assuriya ya ci Samariya, ya kwashe Isra'ilawa zuwa Assuriya, ya ajiye su a Hala, da Habor a bakin kogin Gozan, da cikin garuruwan Mediyawa.

7. Wannan abu ya sami Isra'ila saboda sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fito da su daga ƙasar Masar, daga hannun Fir'auna, Sarkin Masar. Suka bauta wa gumaka.

8. Suka bi al'adun al'ummai waɗanda Ubangiji ya kora a gabansu, da al'adun da sarakunan Isra'ila suka kawo.

9. Jama'ar Isra'ila kuma suka yi wa Ubangiji Allahnsu abubuwan da ba daidai ba, daga ɓoye. Sun gina wa kansu matsafai a dukan garuruwansu daga hasumiya zuwa birni mai garu.

10. Suka kuma kafa wa kansu ginshiƙai da siffofin gumakan Ashtarot a kowane tudu da a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa.

11. Suka ƙona turare a kan wuraren tsafi na kan tuddai kamar yadda al'ummar da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka aikata mugayen abubuwa, suka su Ubangiji ya yi fushi.

12. Suka bauta wa gumaka waɗanda Ubangiji ya ce musu kada su bauta musu.

13. Amma Ubangiji ya faɗakar da jama'ar Isra'ila da jama'ar Yahuza ta bakin annabawa da kowane maigani, cewa su bar mugayen hanyoyinsu, su kiyaye umarnansa da dukan dokokinsa waɗanda ya umarci kakanninsu da su, waɗanda kuma ya aiko musu ta wurin bayinsa annabawa.

14. Duk da haka suka ƙi kasa kunne, suka taurare zuciyarsu kamar yadda kakanninsu suka yi, waɗanda ba su yi imani da Ubangiji Allahnsu ba.

15. Suka yi watsi da dokokinsa, da alkawarinsa da ya yi wa kakanninsu, da kuma faɗakarwar da ya yi musu. Suka bi gumakan banza, suka zama banza, suka bi halin al'ummai da suke kewaye da su, waɗanda Ubangiji ya umarce su kada su yi kamarsu.

16. Suka bar dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu siffofin zubi na 'yan maruƙa biyu, suka yi gunkiyan nan, Ashtoret, suka yi wa taurari sujada, suka bauta wa Ba'al.

17. Suka yi hadaya ta ƙonawa da 'ya'yansu mata da maza. Suka yi duba, suka yi sihiri, suka duƙufa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji, suka sa shi ya yi fushi.

18. Saboda wannan Ubangiji ya husata da jama'ar Isra'ila, ya kawar da su daga gabansa, ba wanda aka rage, sai dai kabilar Yahuza.

19. Jama'ar Yahuza kuma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba, sai suka bi al'adun da mutanen Isra'ila suka kawo.

20. Ubangiji kuwa ya ƙi dukan zuriyar Isra'ila, ya wahalshe su, ya kuma bashe su a hannun mugayen abokan gāba, ta haka ya kawar da su daga gabansa.

21. Sa'ad da Ubangiji ya ɓalle Isra'ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat ya zama sarki. Yerobowam kuwa ya karkatar da jama'ar Isra'ila daga bin Ubangiji. Ya sa su suka aikata babban zunubi.

22. Jama'ar Isra'ila suka yi ta aikata dukan zunuban da Yerobowam ya yi, ba su daina aikata su ba.

23. har lokacin da Ubangiji ya kawar da su daga gabansa kamar yadda ya faɗa ta bakin bayinsa, annabawa. Saboda haka aka fitar da jama'ar Isra'ila daga ƙasarsu zuwa Assuriya har wa yau.

An Zaunar da Assuriyawa cikin Isra'ilawa

24. Sarkin Assuriya kuwa ya kawo mutane daga Babila, da Kuta, da Awwa, da Hamat, da Sefarwayim, ya zaunar da su a garuruwan Samariya a maimakon jama'ar Isra'ila. Sai suka mallaki Samariya, suka zauna a garuruwanta.

25. A farkon zamansu a can, ba su yi tsoron Ubangiji ba saboda haka Ubangiji ya aika da zakoki a cikinsu, suka karkashe waɗansu daga cikinsu.

26. Sai aka faɗa wa Sarkin Assuriya cewa, “Al'umman da ka kwashe ka zaunar da su a garuruwan Samariya ba su san shari'ar Allahn ƙasar ba, domin haka ya aiki zakoki a cikinsu, suna ta karkashe su.”

27. Sa'an nan Sarkin Assuriya ya umarta a aiki firist ɗaya daga cikin firistocin da aka kwashe daga can, ya tafi, ya zauna can domin ya koya musu shari'ar Allahn ƙasar.

28. Sai firist ɗaya daga cikin firistocin da suka kwashe daga Samariya, ya zo, ya zauna a Betel. Shi kuwa ya koya musu yadda za su yi tsoron Ubangiji.

29. Amma duk da haka kowace al'umma ta riƙa yin gumakanta, tana ajiye su a wuraren yin tsafin na kan tuddai waɗanda Samariyawa suka gina. Kowace al'umma kuma ta yi haka a garin da ta zauna.

30. Mutanen Babila suka yi Sukkot-benot, mutanen Kuta suka yi Nergal, mutanen Hamat suka yi Ashima.

31. Awwiyawa suka yi Nibhaz da Tartak, mutanen Sefarwayim suka miƙa 'ya'yansu hadaya ta ƙonawa ga Adrammelek da Anammelek, gumakansu.

32. Su ma suka yi tsoron Ubangiji, suka sa mutane iri dabam dabam su zama firistocin wuraren tsafinsu na kan tuddai. Firistocin nan suka miƙa hadayu dominsu a ɗakunan tsafinsu na kan tuddai.

33. Waɗannan mutane su ma suka yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka bauta wa gumakansu ta hanyar da al'umman da aka kwaso su daga cikinsu suke yi.

34. Har wa yau suna yin yadda suka yi a dā. Ba su yi tsoron Ubangiji ba, ba su bi dokoki, ko ka'idodi, ko shari'a, ko umarnan Ubangiji ba, waɗanda ya umarci 'ya'yan Yakubu, wanda ya sa wa suna Isra'ila.

35. Ubangiji ya yi alkawari da 'ya'yan Yakubu, ya kuma umarce su kada su yi wa gumaka sujada ko su durƙusa musu, ko su bauta musu, ko su miƙa musu hadayu.

36. Amma su yi tsoron Ubangiji, wanda ya fisshe su daga ƙasar Masar da iko mai girma da ƙarfi, shi za su yi wa sujada, shi kuma za su miƙa wa hadayu.

37. Sai su yi biyayya da dokokinsa da umarnansa da ya rubuta musu. Kada su ji tsoron waɗansu alloli.

38. Kada su manta da alkawarin da ya yi da su, kada kuma su ji tsoron gumaka.

39. Amma su yi tsoron Ubangiji Allahnsu, shi kuwa zai cece su daga hannun dukan abokan gābansu.

40. Duk da haka ba su kasa kunne ba, amma suka yi kamar yadda suka saba yi tun dā.

41. Waɗannan al'ummai suka yi wa Ubangiji sujada, amma suka kuma yi ta bauta wa gumakansu. Haka kuma 'ya'yansu da jikokinsu suka yi kamar yadda kakanninsu suka yi. Haka suke yi har wa yau.