Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ezra 8:25-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Na auna musu azurfa, da zinariya, da kwanoni waɗanda sarki da fādawansa, da manyan mutanensa, da Isra'ilawa duka suka kawo suka miƙa domin Haikalin Allahnmu.

26-27. Ga abin da na auna na ba su,talanti ɗari shida da hamsin na azurfakayan azurfa na talanti ɗarikayan zinariya na talanti ɗarikwanonin zinariya guda ashirin na darik dubu (1,000)kwanoni guda biyu na tatacciyar tagulla, darajarsu daidai da kwanon zinariya.

28. Na ce musu, “Ku tsarkaka ne ga Ubangiji, kayayyakin kuma tsarkaka ne, azurfa da zinariya sadaka ce ta yardar rai ga Ubangiji Allah na kakanninku.

29. Ku riƙe su, ku yi tsaronsu, har lokacin da za ku kai su a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin gidajen kakanninku na Isra'ila a Urushalima, a shirayin Haikalin Ubangiji.”

30. Sai firistoci da Lawiyawa suka ɗauki azurfa, da zinariya, da kwanoni waɗanda aka auna, zuwa Urushalima, zuwa Haikalin Allahnmu.

Karanta cikakken babi Ezra 8