Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 14:6-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Jakunan jeji suna tsaye a kan tuddanda ba ciyawa,Suna haki kamar diloli,Idanunsu ba su ganiDomin ba abinci.”

7. Irmiya ya ce,“Ko da yake zunubanmu su neshaidunmu,Ya Ubangiji, ka yi taimako sabodasunanka!Gama kāsawarmu ta yi yawa,Domin mun yi maka zunubi.

8. Ya kai, wanda kake begen Isra'ila,Mai Cetonta a lokacin wahala,Ƙaƙa ka zama kamar baƙo a ƙasar?Kamar matafiyi wanda ya kafaalfarwarsa a gefen hanya don yakwana, ya wuce?

9. Ƙaƙa ka zama kamar wanda bai sanabin da zai yi ba,Kamar jarumin da ya kasa yinceto?Duk da haka, ya Ubangiji, kana nana tsakiyarmu.Da sunanka ake kiranmu,Kada ka bar mu!”

10. Haka Ubangiji ya ce a kan waɗannan mutane, “Sun cika son yawaceyawace, ba su iya zama wuri ɗaya, don haka ni Ubangiji, ban yarda da su ba, zan tuna da laifofinsu in hukunta zunubansu.”

11. Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu'a domin lafiyar jama'an nan.

12. Ko da sun yi azumi, ba zan ji kukansu ba, ko da sun miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta sha, ba zan karɓe su ba. Amma zan hallaka su da takobi, da yunwa, da annoba.”

Karanta cikakken babi Irm 14