Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 4:7-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Sai su shimfiɗa shuɗin zane a kan tebur na gurasar ajiyewa, sa'an nan su dībiya farantai, da cokula, da kwanonin, da butocin hadaya ta sha, da gurasar ajiyewa.

8. Sa'an nan su rufe su da jan zane, a kuma rufe su da fatun awaki, sa'an nan su zura masa sandunansa.

9. Su kuma ɗauki shuɗin zane su rufe alkuki, da fitilunsa, da hantsukansa, da farantansa, da dukan kwanonin man da akan zuba masa.

10. Sai su sa alkukin da dukan kayayyakinsa a cikin fatar awaki su naɗe, su sarƙafa shi asandan ɗaukarsa.

11. A rufe bagaden zinariya da shuɗin zane, a kuma rufe shi da fatun awaki, sa'an nan a zura sandunan ɗaukarsa.

12. Su ɗauki dukan kwanonin da ake amfani da su a Wuri Mai Tsarki, su sa su cikin shuɗin zane, sa'an nan su rufe su da fatun awaki, a sarƙafa su a sanda don a ɗauka.

13. Za su kwashe tokar da take cikin bagaden, su rufe bagaden da shunayyan zane.

14. Sa'an nan su sa dukan kayayyakin bagaden a kansa waɗanda ake aiki da su a wurin, wato su farantai don wuta, da cokula masu yatsotsi, da manyan cokula, da daruna da dai dukan kayayyakin bagaden. Su kuma rufe bagaden da fatun awaki, sa'an nan su zura sandunan ɗaukarsa.

15. Sa'ad da Haruna da 'ya'yansa maza suka gama kintsa Wuri Mai Tsarki da kayayyakinsa duka a lokacin tashi, sai 'ya'yan Kohat, maza, su zo su ɗauke kayayyakin, amma kada su taɓa abubuwan nan masu tsarki domin kada su mutu.Waɗannan su ne ayyukan 'ya'yan Kohat a duk lokacin da za a naɗe alfarwa ta sujada.

16. Ele'azara kuwa, ɗan Haruna, firist, shi ne zai lura da man fitila, da turare, da hadayar gari ta kullum, da man keɓewa, ya kuma kula da dukan alfarwar, da duk abin da yake cikinta, da Wuri Mai Tsarki, da kayayyakinsa.

17. Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,

18. “Kada ku bar zuriyar Kohat

19. ta hallaka ta wurin kusatar waɗannan tsarkakakkun abubuwa. Maganin abin, shi ne sai Haruna da 'ya'yansa maza, su shiga, su nuna wa kowannensu irin aikin da zai yi, da kayan da zai ɗauka.

20. Amma idan Kohatawa suka shiga alfarwar suka tarar firistoci suna shisshirya tsarkakakkun abubuwa don tashi, har dai in sun gani, to za su mutu.”

21. Ubangiji ya kuma faɗa wa Musa,

Karanta cikakken babi L. Kid 4