Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 45:5-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. “Ni ne Ubangiji, ba wani Allah sai ni.Zan ba ka irin ƙarfin da kake bukata,Ko da yake kai ba ka san ni ba.

6. Na yi wannan domin dukan waɗanda suke daga wannan bangon duniya zuwa wancanSu sani ni ne Ubangiji,Ba kuwa wani Allah sai ni.

7. Ni na halicci haske duk da duhu,Ni ne na kawo albarka duk da la'ana.Ni Ubangiji, na yi dukkan waɗannan abu.

8. Zan aiko da nasara daga sararin sama kamar ruwan sama.Ƙasa za ta buɗe ta karɓe ta,Za ta kuwa hudo da 'yanci da gaskiya.Ni Ubangiji, ni zan sa haka ya faru.”

9. Ko tukunyar yumɓu tana iya gardama da magininta,Tukunyar da take daidai da sauran tukwane?Ko yumɓu ya iya tambayar abin da maginin yake yi?Ko tukunya tana iya gunaguni a kan magininta?

10. Ko akwai wanda zai iya ce wa iyayensa,“Don me kuka haife ni kamar haka?”

11. Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila,Shi wanda ya halicce su, ya ce,“Ba ka da iko ka yi mini tambaya game da 'ya'yana,Ko ka faɗa mini abin da ya kamata in yi!

12. Ni ne wanda ya halicci duniya,Na kuma halicci mutum don ya zauna cikinta.Da ikona na shimfiɗa sammai,Ina kuwa mallakar rana, da wata, da taurari.

13. Ni kaina na iza Sairus ya yi wani abu,Don ya cika nufina ya daidaita al'amura.Zan miƙar da kowace hanyar da zai yi tafiya a kai.Zai sāke gina birnina, wato Urushalima,Ya kuma 'yantar da mutanena da suke bautar talala.Ba wanda ya yi ijara da shi, ko ya ba shi rashawa don ya yi wannan.”Ubangiji Mai Runduna ne ya faɗi wannan.

14. Ubangiji ya ce wa Isra'ila,“Dukiyar Masar da ta Habasha za ta zama taku,Dogayen mutanen Seba kuma za su zama bayinku,Za su bi ku suna a ɗaure da sarƙoƙi.Za su rusuna a gabanku su tuba, su ce,‘Allah yana tare da ku, shi kaɗai ne Allah.’ ”

15. Allah na Isra'ila, wanda ya ceci mutanensa,Shi ne yakan ɓoye kansa.

16. Su waɗanda suka yi gumaka, dukansu za su sha kunya,Dukansu za su zama abin kunya.

17. Amma Ubangiji ya ceci Isra'ila,Nasararsa kuwa za ta tabbata har abada,Mutanensa ba za su taɓa shan kunya ba.

18. Ubangiji ne ya halicci sammai,Shi ne wanda yake Allah!Shi ne ya shata duniya ya kuma yi ta,Ya kafa ta, ta kahu da ƙarfi, za ta yi ƙarƙo!Bai halicce ta hamada da ba kome a ciki ba,Amma wurin zaman mutane.Shi ne wanda ya ce, “Ni ne Ubangiji,Ba kuwa wani Allah, sai ni.

Karanta cikakken babi Ish 45