Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 33:29-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na mai da ƙasar kufai marar amfani saboda dukan ayyukansu na banƙyama.” ’ ”

30. Ubangiji ya ce, “Ɗan mutum, mutanenka sun taru a kan garu da cikin ƙofofin gidaje, suna magana da juna a kanka cewa, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’

31. Sukan zo wurinka su zauna, sai ka ce su mutanena ne, sukan ji abin da ka ce, amma ba za su aikata ba, gama suna nuna ƙauna da baka, amma sun ƙwallafa zuciyarsu a kan ƙazamar riba.

32. A gare su ka zama gwanin kiɗa da waƙa, gama suna so su ji abin da kake faɗa, amma ba za su aikata ba.

33. Sa'ad da abin da kake faɗa ya cika [ba shakka kuwa zai cika], sa'an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”

Karanta cikakken babi Ez 33