Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 20:7-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Sai na ce musu, ‘Bari kowane ɗayanku ya yi watsi da abubuwan banƙyama da kuke jin daɗinsu, kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masarawa, gama ni ne Ubangiji Allahnku.’

8. Amma suka tayar mini, ba su ji ni ba, ba su yi watsi da abubuwan banƙyama da suke jin daɗinsu ba, ba su rabu da gumakan Masarawa ba. Sai na ce zan zubo musu da hasalata, in aukar musu da fushina a ƙasar Masar.

9. Amma saboda sunana ban yi wannan ba, domin kada a saɓi sunana cikin sauran al'umma inda mutanen Isra'ila suke zaune, gama na sanar da kaina ga mutanen Isra'ila, a gaban sauran al'umma kuma, sa'ad da na fito da mutanen Isra'ila, daga ƙasar Masar.

10. “Sai na fisshe su daga ƙasar Masar, na kawo su cikin jeji.

11. Na ba su dokokina da ka'idodina, waɗanda idan mutum ya kiyaye su, zai rayu.

12. Na kuma ba su ranar Asabar don ta zama alama tsakanina da su, don kuma su sani ni ne Ubangiji wanda yake tsarkake su.

13. Amma mutanen Isra'ila suka tayar mini a cikin jeji, ba su bi dokokina da ka'idodina ba, waɗanda idan mutum ya kiyaye su, zai rayu. Suka ɓata ranar Asabar ƙwarai. Sai na ce zan zubo musu da hasalata, in aukar da fushina a kansu.

14. Amma saboda sunana ban yi wannan ba, domin kada a saɓi sunana a cikin sauran al'umma waɗanda a kan idonsu na fisshe su.

15. Na kuma rantse musu a cikin jeji, cewa ba zan kai su ƙasar da na ba su ba, ƙasar da take cike da yalwar albarka, wato ƙasar da take mafi albarka duka,

16. domin sun ƙi su bi ka'idodina da dokokina. Suka ɓata ranar Asabar ɗina, gama zuciyarsu ta fi so ta bauta wa gumaka.

Karanta cikakken babi Ez 20