Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

2 Sam 16:2-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Sarki kuwa ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo abubuwan nan?”Ziba ya amsa, ya ce, “An kawo wa iyalin sarki jakuna su hau, da abinci, da 'ya'yan itace, domin samari su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suke rafkewa a jejin su sha.”

3. Sarki kuma ya tambaye shi, “Ina ɗan ubangijinka?”Sai Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima, yana cewa, ‘Yanzu dai mutanen gidan Isra'ila za su mayar mini da sarautar tsohona.’ ”

4. Da jin haka sai sarki ya ce wa Ziba, “Dukan abin da yake na Mefiboshet ya zama naka.”Ziba kuma ya rusuna ya yi godiya ya ce, “Bari in zama majidaɗin ubangijina, sarki.”

5. Sa'ad da Dawuda ya kai Bahurim, sai ga wani mutum sunansa Shimai, ɗan Gera, daga iyalin gidan Saul, ya fito yana ta zagi.

Karanta cikakken babi 2 Sam 16